Home Labarai Gwamnatin Kano na cikin jihohin da suka ciyo bashin naira biliyan 226

Gwamnatin Kano na cikin jihohin da suka ciyo bashin naira biliyan 226

Hukumar kula da bashi ta Najeriya ta ce a cikin wata shida sababbin gwamnonin jihohi 13 na ƙasar ciki har da Kano, da Zamfara, da Katsina sun ci bashin naira biliyan 226 daga masu bayar da bashi a ciki da wajen ƙasar.

Gwamnonin jihohin na daga cikin gwamnoni 16 na ƙasar da suka ci bashin bayan rantsar da su a kan mulki a cikin watan Mayun 2023, inda hukumar kula da basukan ƙasar ta ce ta haɗa al’ƙaluman ne bayan jumlar lissafin da suka yi kan farashin dala a kan naira 889.

Hakan dai na ƙunshe a cikin wani rohoto da ta wallafa a shafinta na internet, inda ta ce an ci bashin ne a tsakanin 30 ga watan Yunin da 30 ga watan Disamba na 2023.

Rohoton da hukumar kula da basukan ta Najeriya ta wallafa ya nuna cewar gwamnoni 16 na ƙasar sun ƙara yawan bashin cikin gida da ake bin jihohinsu da naira biliyan 509, yayin da na ƙetare ya kai naira biliyan 243 da miliyan 95, da kusan dala miliyan 300 kwatankwacin naira biliyan 265 da miliyan 37.

Jihohin da suka ci wannan bashi sun haɗa da Katsina, da Zamfara, da Filato, da Naija, da Benue, da Cross River da babban binrin ƙasar Abuja.

Kuma ana binsu bashin cikin gida na naira billiyan 115,57. Yayin da jihohin Kano, da Kaduna, da Niger, da Filato, da Sokoto, da Taraba, da Zamfara, sai Ebonyi da suka ci bashi daga wajen ƙasar da ya kai dala miliyan 125, dai dai da naira biliyan 111, da miliyan 24.

Hukumar dai ta ce basukan da aka ci a cikin gida su ne aka karbo daga masu bayar da bashi da ke Najeriya, yayin da na ƙetare kuma su ne, wadanda aka ci daga bankin duniya, da na bayar da lamuni na duniya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp