Home Labarai Gwamnatin Kano na cikin jihohin da suka ciyo bashin naira biliyan 226

Gwamnatin Kano na cikin jihohin da suka ciyo bashin naira biliyan 226

Hukumar kula da bashi ta Najeriya ta ce a cikin wata shida sababbin gwamnonin jihohi 13 na ƙasar ciki har da Kano, da Zamfara, da Katsina sun ci bashin naira biliyan 226 daga masu bayar da bashi a ciki da wajen ƙasar.

Gwamnonin jihohin na daga cikin gwamnoni 16 na ƙasar da suka ci bashin bayan rantsar da su a kan mulki a cikin watan Mayun 2023, inda hukumar kula da basukan ƙasar ta ce ta haɗa al’ƙaluman ne bayan jumlar lissafin da suka yi kan farashin dala a kan naira 889.

Hakan dai na ƙunshe a cikin wani rohoto da ta wallafa a shafinta na internet, inda ta ce an ci bashin ne a tsakanin 30 ga watan Yunin da 30 ga watan Disamba na 2023.

Rohoton da hukumar kula da basukan ta Najeriya ta wallafa ya nuna cewar gwamnoni 16 na ƙasar sun ƙara yawan bashin cikin gida da ake bin jihohinsu da naira biliyan 509, yayin da na ƙetare ya kai naira biliyan 243 da miliyan 95, da kusan dala miliyan 300 kwatankwacin naira biliyan 265 da miliyan 37.

Jihohin da suka ci wannan bashi sun haɗa da Katsina, da Zamfara, da Filato, da Naija, da Benue, da Cross River da babban binrin ƙasar Abuja.

Kuma ana binsu bashin cikin gida na naira billiyan 115,57. Yayin da jihohin Kano, da Kaduna, da Niger, da Filato, da Sokoto, da Taraba, da Zamfara, sai Ebonyi da suka ci bashi daga wajen ƙasar da ya kai dala miliyan 125, dai dai da naira biliyan 111, da miliyan 24.

Hukumar dai ta ce basukan da aka ci a cikin gida su ne aka karbo daga masu bayar da bashi da ke Najeriya, yayin da na ƙetare kuma su ne, wadanda aka ci daga bankin duniya, da na bayar da lamuni na duniya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp