Home Labarai Janye Tallafin Lantarki ka iya jefa ‘yan Nijeriya mawuyacin hali

Janye Tallafin Lantarki ka iya jefa ‘yan Nijeriya mawuyacin hali

Al’ummar Najeriya za su fuskanci karin kudin lantarki muddin gwamnati ta ci gaba a kan shirinta na janye tallafi da kashi 15 cikin 100.

Yin hakan zai kara jefa al’ummar kasar cikin mawuyacin hali bisa la’akari da hakin da ake ciki na matsin tattalin arziki.

A ranar Talata ne mai magana da yawun shugaban kasar Bayo Onanuga ya sanar da shirin gwamnatin, yana mai cewa za a yi hakan ne domin a rage kashe kudaden gwamnati.

Idan aka dauki wannan mataki za a rage kashe kudaden gwamnati da kusan dala biliyan biyu da miliyan dari shida.

Ba dai a bayyana lokacin da gwamnati za ta janye tallafin kashi 15 cikin 100 ba.

Ko a yanzu ma ba kowa ba ne yake iya sayen wutar saboda yadda ta yi tsada duk da cewa farashin ya banbanta daga gari zuwa gari da kuma atsakanin unguwanni.

Cire wannan tallafi na nufin wuta za ta koma hannun ‘yan kasuwa kacokan. To sai dai har kawo yanzu kusan fiye da kaso 70 na ‘yan Najeriya ba su da mitar da ake sanyawa kudi.

A kwanakin baya ne dai asusun lamuni na duniya ya shawarci Najeriya da ta cire tallafin mai kacokan da kuma tallafin da take bai wa ‘yan kasar a wutar lantarki.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp