Home DUNIYA Amurka na ganawa da gwamnatin Nijar kan janye dakarunta daga kasar

Amurka na ganawa da gwamnatin Nijar kan janye dakarunta daga kasar

Amurka ta ce jami’anta na ganawa da sojojin da ke mulki a Jamhuriyar Nijar domin tattaunawa game da batun janye sojojinta daga Nijar ɗin.

Hakan ya zo sakamakon makonni da gamayyar ƙungiyar farar hula a Nijar ta shafe tana zanga-zangar goyon bayan juyin mulkin da aka yi a ƙasar ranar 26 ga watan Yuli.

“Jakadiyar Amurka a Nijar, Kathleen FitzGibbon da Manjo Janar Ken Ekman, Daraktan tsare-tsare da tattaunawa na rundunar tsaro ta Amurka da Afirka za su gana da mambobin Majalisar Tabbatar da Tsaron Ƙasa (CNSP) da ke Yamai,” in ji wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fitar.

A mako mai zuwa ne, wasu jami’an tsaron Amurka za su kai ziyara Yamai domin tsara yadda za a kwashe sojojin ƙasar cikin mutunci da gaskiya.

A cewar wata sanarwa, gwamnatin Amurka za ta ci gaba da goyon bayan al’ummar Nijar yayin da suke ƙoƙarin fatattakar mayaƙa.

Sanarwar ta kuma ce mataimakin sakataren harkokin waje, Kurt M. Campbell zai je Yamai a watanni masu zuwa domin tattauna batun yin haɗin gwiwa a batutuwan da buƙatarsu ta zo ɗaya.

Sojojin Nijar sun sanar da kawo ƙarshen yarjejeniyar tsaro da Amurka yayin da ƙasar ke ci gaba da fuskantar ƙaruwar matsalar tsaro da hare-hare daga ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi.

Magoya bayan gwamnatin sojoji a Nijar sun ce kasancewar sojoji har da na Amurka da Faransa ba ya tasiri ga tsaron ƙasar.

A yanzu, sojojin sun ƙulla yarjejeniya da Rasha, a wani mataki da zai faɗaɗa tasirin Moscwo a Afrika.

A makon da ya gabata ne, ƙwararrun sojojin Rasha suka isa Yamai domin horas da dakarun Nijar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp