Home Labarai ‘Yan sandan a Kano sun kama masu kwacen waya

‘Yan sandan a Kano sun kama masu kwacen waya

Rundunar ƴan sanda a jihar Kano ta tabbatar da kama matasa hudu da take zargi da yiwa mutane kwacen waya a jihar.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, wadda ta ce an kama mutanen kan titin Airport Road inda kuma aka same su da wayoyin hannu guda bakwai da ankwa.

Mutanen da ake zargi sun bayyana cewa suna amfani da babur mai ƙafa uku wajen yi wa jama’a ƙwacen waya.

Rundunar ta ce wani Aminu Sulaiman ya shigar da ƙorafi cewa an sace wayarsa cikin motarsa a wani gidan mai da ke jihar inda bayan samun rahoton, wata tawagar ƴan sanda ta kama mutane uku da ake zargi. An gano wayar da aka sace da kuma babur mai ƙafa uku da suke amfani da shi wajen aikata ta’asar.

A cewar rundunar a ranar 23 ga watan Afrilu, sun samu kiran waya inda aka sanar da su wasu ɓatagari a kan babur mai ƙafa uku suna far wa fasinja tare da sace wayarsa. An kuma aika tawagar ƴan sanda inda suka fara bincike sannan suka kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi tare da gano wayar da wuƙa mai kaifi daga wajensa.

Rundunar ta ce ana gudanar da bincike kan mutanen da ake zargi a sashen binciken manyan laifuka sannan daga bisani za a gabatar da su gaban kotu.

Abdullahi kiyawa facebook Page
Abdullahi kiyawa facebook Page

Abdullahi kiyawa facebook Page

Ko dai a ranar bikin hawan Nasarawa da aka gudanar cikin bukukuwan karamar sallah a jihar, Gwamna Abba kabir Yusuf ta cikin jawabinsa ya zargi wasu cikin ‘yan siyasa da bayar da gudunmawa wajen haifar da fadan daba da rikicin siyasa a jihar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp