Home Labarai ‘Yan sandan a Kano sun kama masu kwacen waya

‘Yan sandan a Kano sun kama masu kwacen waya

Rundunar ƴan sanda a jihar Kano ta tabbatar da kama matasa hudu da take zargi da yiwa mutane kwacen waya a jihar.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, wadda ta ce an kama mutanen kan titin Airport Road inda kuma aka same su da wayoyin hannu guda bakwai da ankwa.

Mutanen da ake zargi sun bayyana cewa suna amfani da babur mai ƙafa uku wajen yi wa jama’a ƙwacen waya.

Rundunar ta ce wani Aminu Sulaiman ya shigar da ƙorafi cewa an sace wayarsa cikin motarsa a wani gidan mai da ke jihar inda bayan samun rahoton, wata tawagar ƴan sanda ta kama mutane uku da ake zargi. An gano wayar da aka sace da kuma babur mai ƙafa uku da suke amfani da shi wajen aikata ta’asar.

A cewar rundunar a ranar 23 ga watan Afrilu, sun samu kiran waya inda aka sanar da su wasu ɓatagari a kan babur mai ƙafa uku suna far wa fasinja tare da sace wayarsa. An kuma aika tawagar ƴan sanda inda suka fara bincike sannan suka kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi tare da gano wayar da wuƙa mai kaifi daga wajensa.

Rundunar ta ce ana gudanar da bincike kan mutanen da ake zargi a sashen binciken manyan laifuka sannan daga bisani za a gabatar da su gaban kotu.

Abdullahi kiyawa facebook Page
Abdullahi kiyawa facebook Page

Abdullahi kiyawa facebook Page

Ko dai a ranar bikin hawan Nasarawa da aka gudanar cikin bukukuwan karamar sallah a jihar, Gwamna Abba kabir Yusuf ta cikin jawabinsa ya zargi wasu cikin ‘yan siyasa da bayar da gudunmawa wajen haifar da fadan daba da rikicin siyasa a jihar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp