Home Labarai ‘Yan sandan a Kano sun kama masu kwacen waya

‘Yan sandan a Kano sun kama masu kwacen waya

Rundunar ƴan sanda a jihar Kano ta tabbatar da kama matasa hudu da take zargi da yiwa mutane kwacen waya a jihar.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, wadda ta ce an kama mutanen kan titin Airport Road inda kuma aka same su da wayoyin hannu guda bakwai da ankwa.

Mutanen da ake zargi sun bayyana cewa suna amfani da babur mai ƙafa uku wajen yi wa jama’a ƙwacen waya.

Rundunar ta ce wani Aminu Sulaiman ya shigar da ƙorafi cewa an sace wayarsa cikin motarsa a wani gidan mai da ke jihar inda bayan samun rahoton, wata tawagar ƴan sanda ta kama mutane uku da ake zargi. An gano wayar da aka sace da kuma babur mai ƙafa uku da suke amfani da shi wajen aikata ta’asar.

A cewar rundunar a ranar 23 ga watan Afrilu, sun samu kiran waya inda aka sanar da su wasu ɓatagari a kan babur mai ƙafa uku suna far wa fasinja tare da sace wayarsa. An kuma aika tawagar ƴan sanda inda suka fara bincike sannan suka kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi tare da gano wayar da wuƙa mai kaifi daga wajensa.

Rundunar ta ce ana gudanar da bincike kan mutanen da ake zargi a sashen binciken manyan laifuka sannan daga bisani za a gabatar da su gaban kotu.

Abdullahi kiyawa facebook Page
Abdullahi kiyawa facebook Page

Abdullahi kiyawa facebook Page

Ko dai a ranar bikin hawan Nasarawa da aka gudanar cikin bukukuwan karamar sallah a jihar, Gwamna Abba kabir Yusuf ta cikin jawabinsa ya zargi wasu cikin ‘yan siyasa da bayar da gudunmawa wajen haifar da fadan daba da rikicin siyasa a jihar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp