Home Labarai Gwamnatin Tinubu tayi karin Albashi ga ma’aikatan Nijeriya

Gwamnatin Tinubu tayi karin Albashi ga ma’aikatan Nijeriya

Gwamnatin tarayya a Najeriya ta yi wa ma’aikatanta ƙarin albashi da kimanin kashi 25 cikin ɗari zuwa kashi 35 cikin ɗari.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin bukin ranar ma’aikata ta duniya.

A ranar Talata ne wata takarda daga shugaban hukumar kula da albashi ta Najeriya, Ekpo Nta ta tabbatar da ƙarin albashin.

Takardar ta nuna cewa ƙarin albashin zai fara ne daga ranar ɗaya ga watan Janairun 2024.

Kamar akasarin al’umma ƙasar, ma’aikatan gwamnati a Najeriya sun faɗa cikin mawuyacin hali sanadiyyar matsin tattalin arziƙi.

Kayan masarufi sun yi tashin gwauron zabi sannan darajar naira ta zube idan aka kwatanta da dalar Amurka duk kuwa da sabbin matakan da gwamnatin ƙasar ke ci gaba da ɗauka.

Yanzu haka akwai wani kwamiti da gwamnatin ƙasar ta kafa wanda ke aiki tare da ƙungiyoyin ƙwadago na ƙasar domin samar da matsaya kan ƙarancin albashi ga ma’aikata a ƙasar.

A baya ƙungiyoyin ƙwadago sun sha yin barazanar shiga yajin aiki da durƙusar da lamurra a ƙasar domin tursasa wa gwamnatin tarayya ɗaukan matakan bunƙasa walwalar ma’aikata.

A halin yanzu mafi ƙarncin albashin ma’aikata a hukumance shi ne naira 30,000.

Kuma duk da haka akasarin gwamnatocin jihohi ba su iya biyan ma’aikatansu albashin mafi ƙaranci, inda akan samu wasu ma’aikata na bin bashin albashin watanni da dama.

Wannan sabon albashin da gwamnatin ta amince da shi zai shafi ma’aikatan gwamnati da ke bisa tsarin CONPSS, da na ma’aikatan kwalejojin bincike na CONRAISS, da jami’an ƴansanda (CONPOSS) da ma’aikatan tattara bayanan sirri (CONICCS) da sauran masu ɗamara (CONPASS) da kuma dakarun ƙasar (CONAFSS).

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp