Home Labarai ‘Yan majalisar wakilai a Nijeriya sun bukaci dakatar shugaban NNPC

‘Yan majalisar wakilai a Nijeriya sun bukaci dakatar shugaban NNPC

Ƴan majalisar wakilai 15 a ƙarkashin ƙungiyar The Economy Rescue Group”, sun nemi da a dakatar da shugaban rukunin kamfanin mai na Nijeriya Mele Kyari.

Ƙungiyar ta yi ikirarin cewa rashin tafiyar da tsare tsare karkashin jagorancin Kyari a NNPC ne ke jawo ƙalubalen da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ke fuskanta.

Wannan na cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar a Abuja kuma shugabanta ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Oredo, Esosa Iyawe, shi ne ya sanya mata hannu kuma aka saki a ranar Talata, inda ƙungiyar ta dage cewa a dakatar da Kyari har sai an samu sakamakon kwamitin hadin gwiwa na majalisar wakilai game da binciken kwakwaf da ake yi na kan harkokin man fetur game da halin da kamfanin mai na kasa ke ciki.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Mu ‘yan majalisa mai ɗauke da mutane 15 mun lura cewa ko shakka babu matsalolin da ake fuskanta a bangaren man fetur da iskar gas a gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya samo asali ne sakamakon gazawa da rashin gudanar da ayyukan hukumar ta NNPC a karkashin jagorancin Kyari. Don haka, don warware waɗannan matsaloli dole ne su yi murabus.

Haka kuma ƴan majalisar na zargin shugaban kamfanin na NNPC da sauran ma’aikatan gudanarwar da yi wa tsarin shugaban kasa na daidaita tattalin arziki mai lakabin “Renewed Hope Agenda” zagon kasa.
“Tunda sun kasa sauka da kansu, to bai kamata shugaban kasa ya yi kasa a gwiwa ba wajen dakatar da su har sai an gama gudanar da binciken da majalisar wakilai ke gudanarwa kan harkokin man fetur.
PRNigeria hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp