Home Labarai ‘Yan majalisar wakilai a Nijeriya sun bukaci dakatar shugaban NNPC

‘Yan majalisar wakilai a Nijeriya sun bukaci dakatar shugaban NNPC

Ƴan majalisar wakilai 15 a ƙarkashin ƙungiyar The Economy Rescue Group”, sun nemi da a dakatar da shugaban rukunin kamfanin mai na Nijeriya Mele Kyari.

Ƙungiyar ta yi ikirarin cewa rashin tafiyar da tsare tsare karkashin jagorancin Kyari a NNPC ne ke jawo ƙalubalen da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ke fuskanta.

Wannan na cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar a Abuja kuma shugabanta ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Oredo, Esosa Iyawe, shi ne ya sanya mata hannu kuma aka saki a ranar Talata, inda ƙungiyar ta dage cewa a dakatar da Kyari har sai an samu sakamakon kwamitin hadin gwiwa na majalisar wakilai game da binciken kwakwaf da ake yi na kan harkokin man fetur game da halin da kamfanin mai na kasa ke ciki.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Mu ‘yan majalisa mai ɗauke da mutane 15 mun lura cewa ko shakka babu matsalolin da ake fuskanta a bangaren man fetur da iskar gas a gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya samo asali ne sakamakon gazawa da rashin gudanar da ayyukan hukumar ta NNPC a karkashin jagorancin Kyari. Don haka, don warware waɗannan matsaloli dole ne su yi murabus.

Haka kuma ƴan majalisar na zargin shugaban kamfanin na NNPC da sauran ma’aikatan gudanarwar da yi wa tsarin shugaban kasa na daidaita tattalin arziki mai lakabin “Renewed Hope Agenda” zagon kasa.
“Tunda sun kasa sauka da kansu, to bai kamata shugaban kasa ya yi kasa a gwiwa ba wajen dakatar da su har sai an gama gudanar da binciken da majalisar wakilai ke gudanarwa kan harkokin man fetur.
PRNigeria hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp