Home Labarai Gwamnatin Kano ta sake shigar da kara kan Ganduje

Gwamnatin Kano ta sake shigar da kara kan Ganduje

Gwamnatin jihar Kano ta shigar da sabuwar kara dake tuhumar tsohon Gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje da Murtala Sule Garo da wasu mutane biyu.

Acewar takardar karar, ana tuhumar Murtala Garo da Lamin Sani da Muhammad Takai da hada kai wajen aikata laifi da zanba cikin aminci da gabatar da bayanan karya da badakalar kudade.

Gwamnatin na zarginsu da wawure kudin kananan hukumomi dake asusun hadaka tsakanin jihar da kananan hukumomi 44.

Sannan ana zargin badakalar kudi ta Naira Biliyan 57.4 da suka karkatar dasu zuwa asusun ajiya na kashin kai.

Haka kuma ana zargin sun sauya kudin zuwa Dalar Amurka.

Haka kuma, gwamnatin na tuhumar su da mallakar kadarori da kudaden a kasar Dubai da Otel a garin Abuja da wasu gidajen mai a Kano.

Gwamnatin dai ta ce zata gabatar da shaidu 143 a gaban kotun a lokacin shari’ar.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp