Home Labarai Gwamnatin Kano ta sake shigar da kara kan Ganduje

Gwamnatin Kano ta sake shigar da kara kan Ganduje

Gwamnatin jihar Kano ta shigar da sabuwar kara dake tuhumar tsohon Gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje da Murtala Sule Garo da wasu mutane biyu.

Acewar takardar karar, ana tuhumar Murtala Garo da Lamin Sani da Muhammad Takai da hada kai wajen aikata laifi da zanba cikin aminci da gabatar da bayanan karya da badakalar kudade.

Gwamnatin na zarginsu da wawure kudin kananan hukumomi dake asusun hadaka tsakanin jihar da kananan hukumomi 44.

Sannan ana zargin badakalar kudi ta Naira Biliyan 57.4 da suka karkatar dasu zuwa asusun ajiya na kashin kai.

Haka kuma ana zargin sun sauya kudin zuwa Dalar Amurka.

Haka kuma, gwamnatin na tuhumar su da mallakar kadarori da kudaden a kasar Dubai da Otel a garin Abuja da wasu gidajen mai a Kano.

Gwamnatin dai ta ce zata gabatar da shaidu 143 a gaban kotun a lokacin shari’ar.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp