Home Labarai NBS- Jihar Kano ta rabauta da sama da biliyan biyun don inganta...

NBS- Jihar Kano ta rabauta da sama da biliyan biyun don inganta muhalli

Jihar Kano ta karbi kaso mai tsoka daga kwamitin rabon arzikin kasa, wanda hakan ya sanya jihar zama kan gaba cikin jihohin kasar 36, a tsakanin watan yunin shekarar 2023, zuwa watan yunin wannan shekara.

Hukumar kididdiga ta kasa NBS ce ta fitar da rahoton dake nuna cewa jihar Kano a tsakanin lokacin ta rabauta da kudi naira Biliyan 2 da milyan daya, domin amfani da kudin wajen magance matsalolin da suka shafi muhalli a jihar.

Daga cikin manufar bayar da kudin gwamnatin tarayya na fatan jihohin kasar suyi amfani da kudin, wajen magance matsalolin muhalli irin su kwararowar hamada, ambaliyar ruwa, da kuma zaizayar kasa.

A yan shekarun da suka gabata, gwamnatin tarayya ta baiwa jihohi naira Biliyan 38.62, wanda kuma jihar Kano ta zama kan gaba wajen karba naira miliyan 175 duk wata domin gudanar da wadancan ayyuka.

Rahoton yace Jihar Borno dake fama da matsalar masu tayar da kaya baya na boko haram da yadda muhalli ya salwanta a wannan jiha, bata kai Kano karbar kaso mai tsoka ba, domin kuwa Borno duk wat ana rabauta da naira Milyan 140 ne kaca, wato Kano ta bata tazarar naira miliyan 35 ke nan a yadda rahoton hukumar NBS ya bayyana.

Sassa da dama yanzu haka na jihar nan na fama da matsalar zaizayar kasa, musamman garin daba dake yankin karamar hukumar Dawakin Kudu, zaizayar kasar dake ci gabar da haifar da koma baya ga manoman yankin kuma a kullum kira suke ga gwamnati amma a cewarsu har yanzu shiru.

Shi dai wannan kudi akan ware kaso 2 cikin dari na arzikin kasa, tare da baiwa ofishin kula da asusun taimakawa muhallin wanda ke karkashin ofishin sakataren gwamnatin tarayya, kuma tun a shekarar 1981 aka fara wannan tsari.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp