Home Labarai Gwamnan Kano ya bayar da umarnin bincikar badakar sayen magunguna a jihar

Gwamnan Kano ya bayar da umarnin bincikar badakar sayen magunguna a jihar

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa bashi da masaniya kan kwangilar samar da magunguna a kananan hukumomi 44 na jihar.

wannan na cikin wata Sanarwar da kwamishinan yada Labarai na jihar Baba Halilu Dan Tiye ya fitar wadda aka rabawa manema labarai, ta ce Gwamnan Abba ya umurci Shugaban Hukumar karbar Korafe-korafe da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano da ta gaggauta bincikar wannan zargi tare da bayar da rahoton sakamakon da ya dace domin daukar matakin da ya dace.

Sanarwar ta ci gaba da cewa manufar binciken shine bankado gaskiyar Lamarin domin tabbar da gaskiya da rikon amana wajen gudanar da shugabanci na gari ga alummar Kano baki daya.

Daga bisani Gwamna Yusuf ya kuma bukaci daukacin al’ummar Kano da su yi hakuri har a kammala bincike.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp