Home General Boko haram ta hallaka Masallata 34 a jihar Yobe

Boko haram ta hallaka Masallata 34 a jihar Yobe

Wani harin mayakan boko haram kan masallata yayi sanadiyyar mutuwar mutane 34, a garuruwan Mafa, Tarmuwa dake jihar Yobe a arewa maso gabashin Nijeriya.

Mayakan na boko haram sun isa wani masallaci yayin da al’umma ke tsaka gudanar da sallah Magriba, in suka ka su da harbin kan mai uwa da wabi a ranar lahadin data gabata.

Mai sharhi kan al’amurarran da suka shafi tsaro a yankin tafkin Chadi Zagazola Makama, ya ruwaito cewa harin na matsayin martanin mayakan boko haram kan Al’ummar yankin bisa kin biyan harajin da suka yi ga kungiyar dake tayar da kayar bayan a yankin.

Yace aboye al’ummar garin na biyan mayakan na boko haram haraji ba tare da sanin jami’an tsaro ba, wannan ne yasa mayakn na boko haram kai musu mummunan harin da yayi sandiyyar mutuwar mutane.

Haka kuma rahoton yace a wani yunkuri na tsananta lamarin mayakan sun binne wasu abubuwan fashewa guda hudu akan hanya domin harar dakarun da zasu kawo dauki bayan sun kamala gudanar da ta’addancin kan Al’ummar.

Wannan harin na boko haram ya sake fito da matsin da suke kara fuskanta a wajen jami’an tsaro, tare da fito da bukatar dake akwai na sake bawa dakarun sojojin bayanan sirrin don dakile ayyukan ‘yan ta’addan.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp