Home General Boko haram ta hallaka Masallata 34 a jihar Yobe

Boko haram ta hallaka Masallata 34 a jihar Yobe

Wani harin mayakan boko haram kan masallata yayi sanadiyyar mutuwar mutane 34, a garuruwan Mafa, Tarmuwa dake jihar Yobe a arewa maso gabashin Nijeriya.

Mayakan na boko haram sun isa wani masallaci yayin da al’umma ke tsaka gudanar da sallah Magriba, in suka ka su da harbin kan mai uwa da wabi a ranar lahadin data gabata.

Mai sharhi kan al’amurarran da suka shafi tsaro a yankin tafkin Chadi Zagazola Makama, ya ruwaito cewa harin na matsayin martanin mayakan boko haram kan Al’ummar yankin bisa kin biyan harajin da suka yi ga kungiyar dake tayar da kayar bayan a yankin.

Yace aboye al’ummar garin na biyan mayakan na boko haram haraji ba tare da sanin jami’an tsaro ba, wannan ne yasa mayakn na boko haram kai musu mummunan harin da yayi sandiyyar mutuwar mutane.

Haka kuma rahoton yace a wani yunkuri na tsananta lamarin mayakan sun binne wasu abubuwan fashewa guda hudu akan hanya domin harar dakarun da zasu kawo dauki bayan sun kamala gudanar da ta’addancin kan Al’ummar.

Wannan harin na boko haram ya sake fito da matsin da suke kara fuskanta a wajen jami’an tsaro, tare da fito da bukatar dake akwai na sake bawa dakarun sojojin bayanan sirrin don dakile ayyukan ‘yan ta’addan.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp