Home General Annobar amai da gudawa ta hallaka mutane bakwai a jihar Jigawa

Annobar amai da gudawa ta hallaka mutane bakwai a jihar Jigawa

Gwamnatin jihar Jigawa dake arewa Maso yammacin kasar ta tabbata da barkewar annobar amai da gudawa a karamar hukumar kirikasamma, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane bakwai tare da kwantar da dama a Asibitin jihar.

Shugaban kula da lafiyar al’umma na yankin na kirikasamma, Musa Abdullahi Diladige ne, ya tabbatar da barkewar cutar a yankunan Malori, Maikintari, Dilmari, Kirikasamma, da wani bangare na kauyen Baturiya.

Diladige, ya bayyana cewa wadanda abin ya shafa na fama da alamomin rashin lafiya masu tsanani kamar gudawa, kumburin ciki, amai, da zazzabi

An tura ma’aikatan lafiya zuwa yankunan don samar da agajin gaggawa.

Hukumomi sun dauki matakin gaggawa ta hanyar sayan magungunan da ake bukata don fara jinyar masu cutar.

Daraktan gudanarwa da ayyukan gama-gari, Idris Gambo Abubakar, ya yi alkawarin bayar da goyon bayan da ake bukata don dakile yaduwar cutar.

Ana kyautata zaton ruwan sama mai tsanani da aka samu a yankin ne ya haifar da barkewar cutar, inda gine-gine suka lalace kuma hanyoyin samar da ruwa suka lalace.

An shawarci mazauna yankin da su dauki matakan kariya nan take.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp