Home General Daurarru na mutuwa saboda yunwa a gidajen yarin Nijeriya

Daurarru na mutuwa saboda yunwa a gidajen yarin Nijeriya

Hukumar dake lura da gidan ajiya da gyaran hali ta Calabar dake jihar cross river ta ce ta na bincike kan  matsalar ciyar da daurarru dake ajje a gidan domin tabbatar da walwalar su.

Kakakin hukumar na jihar Abubakar Umar ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da kamfanin dillanci labarai na Nijeriya NAN a birnin Abuja ranar talata.

Inda yace ministan cikin gida na Olubunmi Tunji-Ojo, ya bayar da umarnin a gudanar da bincike kan zargin badakala a harkokin ciyar da daurarru a gidan ajiya da gyaran hali na Afokang dake tsakiyar Calabar a jihar Cross River.

Umarnin na zuwa ne bayan wani faifan bidiyo daya fito kan yadda ake lura da daurarrun, wanda ciki harda yadda ake basu wani wake da bai dahu ba a lokacin Karin kumallo.

Ko dai ta cikin wani sako da Dan jarida Ja’afar Ja’afar Ya wallafa a shafinsa na facebook ya bayyana yadda wani ma’aikacin gidan gyaran hali da tarbiyya ya aike masa da wani sako kan halin da daurarru ke ciki a gidan ajiya da gyaran hali.

Sakon yace “Sir mutane na mutuwa a Prison saboda yunwa” “Wallahi a inda nake aiki kullum sai an fita da gawa” “kuma Yunwa ce”.

“sun hana kowa shiga da Phone (waya) don kada a dauki hoton abinci”

“hoton dake yawo na calaba Prison to kusan duk sauran prison din haka suke babu abinci”

“Staff wani lokacin ke taimakon Inmate da abinci da ga cikin salary su” “wallahi ko ni kusan duk sati sai na sayi kuli-kuli da garin rogo na rabawa inmate”.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp