Home General Daurarru na mutuwa saboda yunwa a gidajen yarin Nijeriya

Daurarru na mutuwa saboda yunwa a gidajen yarin Nijeriya

Hukumar dake lura da gidan ajiya da gyaran hali ta Calabar dake jihar cross river ta ce ta na bincike kan  matsalar ciyar da daurarru dake ajje a gidan domin tabbatar da walwalar su.

Kakakin hukumar na jihar Abubakar Umar ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da kamfanin dillanci labarai na Nijeriya NAN a birnin Abuja ranar talata.

Inda yace ministan cikin gida na Olubunmi Tunji-Ojo, ya bayar da umarnin a gudanar da bincike kan zargin badakala a harkokin ciyar da daurarru a gidan ajiya da gyaran hali na Afokang dake tsakiyar Calabar a jihar Cross River.

Umarnin na zuwa ne bayan wani faifan bidiyo daya fito kan yadda ake lura da daurarrun, wanda ciki harda yadda ake basu wani wake da bai dahu ba a lokacin Karin kumallo.

Ko dai ta cikin wani sako da Dan jarida Ja’afar Ja’afar Ya wallafa a shafinsa na facebook ya bayyana yadda wani ma’aikacin gidan gyaran hali da tarbiyya ya aike masa da wani sako kan halin da daurarru ke ciki a gidan ajiya da gyaran hali.

Sakon yace “Sir mutane na mutuwa a Prison saboda yunwa” “Wallahi a inda nake aiki kullum sai an fita da gawa” “kuma Yunwa ce”.

“sun hana kowa shiga da Phone (waya) don kada a dauki hoton abinci”

“hoton dake yawo na calaba Prison to kusan duk sauran prison din haka suke babu abinci”

“Staff wani lokacin ke taimakon Inmate da abinci da ga cikin salary su” “wallahi ko ni kusan duk sati sai na sayi kuli-kuli da garin rogo na rabawa inmate”.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp