Home General Muna ɗaukar matakai masu tsauri ne don gina ƙasarmu- Tinubu

Muna ɗaukar matakai masu tsauri ne don gina ƙasarmu- Tinubu

Bola Ahned Tinubu

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na ɗaukar matakai masu tsauri ne domin gina ƙasar tare da samar mata ingantaccen ci gaba.

Yayin da yake jawabi ga ƙungiyar ‘yan asalin Najeriya mazauna China, a birnin Beijing, Shugaba Tinubu ya ce an ƙara farashin man fetur ne a ƙasar, domin samar wa Najeriya ingantaccen ci gaba.

”Za ku ji a ‘yan kwanakin nan ana ta magana game da ƙarin kuɗin man fetur, amma magana ta gaskiya za mu iya gina ƙasarmu? Mu samu tituna masu kyau kamar yadda muka gani a nan (China), mu samu tsayayyiyar wutar lantarki da ruwan sha, kuma kun dai ga yadda makarantunsu ke da kyau a nan”, in ji Tinubu.

Ya ƙara da cewa ”idan muna son cimma waɗannan abubuwa sai mun ɗauki matakai masu tsauri domin samun hanyar da za ta kai mu ga ciyar da ƙasarmu gaba”.

Shugaban ƙasar ya ce ba a samun kowane irin ci gaba cikin sauƙi ko kuma a ɓagas.

“Idan kana son ka samu komai a kyauta, to zai zame maka mai wahalar samu ko ka jima ba ka same shi ba”, in ji shugaban na Najeriya.

”Kalli tituna masu kyau da inganci a nan, ina so na kwaikwayi irin waɗannan ayyuka a Najeriya, ina son gyara makarantun ‘ya’yanmu, bana son ganin ɗalibanmu suna zama a azuzuwan da suka lalace, ina son gayar tsarin koyarwa”, in ji shi.

A ranar Talata ne dai babban kamfanin mai na asar NNPCL ya sanar da ƙarin kuɗin man fetur zuwa naira 855, dangane da inda mutum ke zaune a ƙasar, lamarin da ya ya janyo wa gwamnatin ƙasar suka daga ƙungiyoyi da ɗaiɗaikun mutane.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp