Home General Jam’iyyar PDP ta yiwa Kwankwaso martani

Jam’iyyar PDP ta yiwa Kwankwaso martani

Jam’iyyar PDP ta mayar da martani kan kalaman da sanata Rabi’u Kwankwaso, dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP a zaɓen 2023 ya yi wanda ya yi iƙirarin cewa jam’iyyar PDP ba ta da wani tasiri a siyasar Najeriya, inda ya ce jam’iyyar ta mutu.

A ranar Asabar ne dai Sanata Kwankwaso yayin buɗe ofishin jam’iyyar NNPP na jihar Katsina, jagoran Kwankwasiyyar ya zargi jam’iyyar PDP da APC mai mulki da jefa kanta cikin abin da ya kira ”halaka”.

A cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran jam’iyyar na ƙasa Debo Ologunagba ya fitar a ranar Lahadi, PDP ta bayyana Kwankwaso a matsayin “mara muhimmanci a siyasar Najeriya” tare da zargin sa da son kai.

Ologunagba, ya soki kalaman Kwankwaso, inda ya nuna cewa jam’iyyar NNPP a karkashin shugabancin Kwankwaso na ƙoƙarin gina kanta ne a jiha ɗaya kacal, yayin da kuma jam’iyyar PDP har yanzu na da tasiri a faɗin jihohi 13 da ke da gagarumin wakilci a majalisar dokokin ƙasar.

Sanarwar ta ce “Rabi’u Kwankwaso ba shi da wani tasiri a siyasar Najeriya a yau idan aka yi la’akari da yadda yake fafutukar ganin ya jagoranci wata jam’iyya mai suna NNPP wadda ita ma ke fafutukar ganin ta gina kanta a jiha ɗaya kawai.”

“Abin da za a fi mayar da hankali a nan shi ne yadda Sanata Kwankwaso ya nuna tsananin son kai, wanda hakan ke nuna cewa shi ba shugaba ba ne.”

PDP ta ce abin mamaki ne yadda Kwankwaso, wanda suka bayyana a matsayin dan siyasar da ya gaza, zai ayyana jam’iyyar da ke da ƙasa baki daya a matsayin ta mutu.

PDP ta kara zargin Kwankwaso da fifita burinsa na siyasa fiye da jin dadin ‘yan Najeriya.

“Shugaba na gaskiya zai mayar da hankali ne wajen magance matsalolin da ke addabar ƙasar maimakon yin kalamai masu kawo raba kan jama’a.” sanarwar ta ƙara da cewa.

Da yake karin haske kan matsalar tattalin arzikin da ake fama da shi a halin yanzu, Ologunagba ya jaddada cewa ‘yan Najeriya na cikin mawuyacin hali a karkashin gwamnatin jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

“Kwankwaso ya fi mayar da hankali kan burinsa na zama shugaban kasa yayin da ‘yan Najeriya ciki har da na jiharsa ta Kano ke fama da yunwa da ƙunci.”

“Sama da mutane miliyan 150 ne suka fada cikin talauci, inda miliyoyi suka rasa abin dogaro da kai, yayin da hauhawar farashin kayayyaki da man fetur suka yi tashin gwauron zabi.” in ji sanarwar.

PDP ta kara da cewa siyasar Kwankwaso ta samo asali ne tun lokacin da ya ke jam’iyyar, kuma abin takaici ne yadda ya ci gaba da mayar da hankali kan burinsa a irin wannan mawuyacin lokaci da kasar ke ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp