Home General Sojojin Najeriya – Mun hallaka ‘ƴan bindiga 792 cikin wata uku

Sojojin Najeriya – Mun hallaka ‘ƴan bindiga 792 cikin wata uku

Hedkwatar tsaron Najeriya ta ce ta hallaka ƴan bindiga kimanin 792 tsakanin watan Yuli zuwa Satumban da muke ciki.

Wannan na cikin wata sanarwa da daraktan yaɗa labaran hedkwatar, Edward Buba ya fitar, in da ya ce dakarun tsaron ƙasar, ƙarƙashin rundunar Operation HADIN KAI ta samu nasarar kai hare-hare cikin dajin Sambisa da na Tumbuns a yankin tafkin Chadi, tare da kashe wasu manyan kwamandojin ‘ƴan bindigar.

Sanarwar ta ƙara da cewa hare-haren da sojojin suka kai wa mayaƙan ya rage musu ƙarfi, tare da hana su ƙaddamar da manya-manyan hare-hare.

Edwar Buba ya ci gaba da cewa a lokacin ayyukan soji a waɗanann yankuna tsakanin waɗannan watanni, dakarun ƙasar sun samu nasarar kashe wasu manyan kwamandojin ƴanbingida da suka haɗa da Munzir Arika da Sani Dilla (Ɗan Hausawan Jubillaram) da Ameer Modu da Ɗan Fulani Fari Fari Dungusu da Abu Darda da Bakoura Arina Chiki da Dungusu da Abu Darda da kuma Abu Rijab.

Haka kuma sanarwar ta ce an kama wasu da ake zargi da kasancewa ƴanbidigar kimanin 606 tsakanin waɗannan watanni tare da kuɓutar da mutum 476 da ake garkuwa da su, sannan kuma wasu iyalan ƴanbindigar kimanin 7,283 suka miƙa wuya.

Sanarwar ta kuma ce dakarun sojin sun ƙwato makamai da suka haɗa da bindiga ƙirar AK47 guda 339, da ƙirar gida 58 da ƙananan bindigogi 83 da kuma tarin alburusai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp