Home General Sojojin Najeriya – Mun hallaka ‘ƴan bindiga 792 cikin wata uku

Sojojin Najeriya – Mun hallaka ‘ƴan bindiga 792 cikin wata uku

Hedkwatar tsaron Najeriya ta ce ta hallaka ƴan bindiga kimanin 792 tsakanin watan Yuli zuwa Satumban da muke ciki.

Wannan na cikin wata sanarwa da daraktan yaɗa labaran hedkwatar, Edward Buba ya fitar, in da ya ce dakarun tsaron ƙasar, ƙarƙashin rundunar Operation HADIN KAI ta samu nasarar kai hare-hare cikin dajin Sambisa da na Tumbuns a yankin tafkin Chadi, tare da kashe wasu manyan kwamandojin ‘ƴan bindigar.

Sanarwar ta ƙara da cewa hare-haren da sojojin suka kai wa mayaƙan ya rage musu ƙarfi, tare da hana su ƙaddamar da manya-manyan hare-hare.

Edwar Buba ya ci gaba da cewa a lokacin ayyukan soji a waɗanann yankuna tsakanin waɗannan watanni, dakarun ƙasar sun samu nasarar kashe wasu manyan kwamandojin ƴanbingida da suka haɗa da Munzir Arika da Sani Dilla (Ɗan Hausawan Jubillaram) da Ameer Modu da Ɗan Fulani Fari Fari Dungusu da Abu Darda da Bakoura Arina Chiki da Dungusu da Abu Darda da kuma Abu Rijab.

Haka kuma sanarwar ta ce an kama wasu da ake zargi da kasancewa ƴanbidigar kimanin 606 tsakanin waɗannan watanni tare da kuɓutar da mutum 476 da ake garkuwa da su, sannan kuma wasu iyalan ƴanbindigar kimanin 7,283 suka miƙa wuya.

Sanarwar ta kuma ce dakarun sojin sun ƙwato makamai da suka haɗa da bindiga ƙirar AK47 guda 339, da ƙirar gida 58 da ƙananan bindigogi 83 da kuma tarin alburusai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp