Home Labarai Najeriya ta yi asarar abincin da zai ciyar da mutum miliyan takwas...

Najeriya ta yi asarar abincin da zai ciyar da mutum miliyan takwas a 2024 – FAO

Hukumar abinci da bunƙasa aikin noma ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce Najeriya ta tafka asarar tan 55,629 na abinci saboda ambaliyar ruwa a 2024.

Ƙididdigar da hukumar ta fitar ta nuna cewa asarar kayan abinci da aka tafka a Najeriya a bana ta isa a ciyar da mutum miyan takwas da rabi har tsawo wata shida.

Mataimakin shugaban hukumar a Najeriya, Salisu Mohammed, ya ce ɗumamar yanayi da hauhawar farashi da matsalar tsaro da kuma taɓarɓarewar tattalin arziki, na daga cikin abubuwan da suka addabi ɓangaren noma a Najeriya cikin shekarar nan.

Wannan ƙididdiga na zuwa ne albarkacin bikin Ranar Abinci ta Duniya, wanda ya mayar da hankali ga kira ga gwamnati ta haɗa hannu da ƙwararru wajen magance ƙalubalen ƙarancin abinci mai gina jiki a tsakanin al’umma.

Hukumar ta bayyana gamsuwa da matakan da gwamnati ke ɗauka wajen wadata ƙasa da abinci, amma ta yi gargaɗin cewa dole sai ta ƙara ƙaimi domin cim ma hakan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp