Home Labarai Najeriya ta yi asarar abincin da zai ciyar da mutum miliyan takwas...

Najeriya ta yi asarar abincin da zai ciyar da mutum miliyan takwas a 2024 – FAO

Hukumar abinci da bunƙasa aikin noma ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce Najeriya ta tafka asarar tan 55,629 na abinci saboda ambaliyar ruwa a 2024.

Ƙididdigar da hukumar ta fitar ta nuna cewa asarar kayan abinci da aka tafka a Najeriya a bana ta isa a ciyar da mutum miyan takwas da rabi har tsawo wata shida.

Mataimakin shugaban hukumar a Najeriya, Salisu Mohammed, ya ce ɗumamar yanayi da hauhawar farashi da matsalar tsaro da kuma taɓarɓarewar tattalin arziki, na daga cikin abubuwan da suka addabi ɓangaren noma a Najeriya cikin shekarar nan.

Wannan ƙididdiga na zuwa ne albarkacin bikin Ranar Abinci ta Duniya, wanda ya mayar da hankali ga kira ga gwamnati ta haɗa hannu da ƙwararru wajen magance ƙalubalen ƙarancin abinci mai gina jiki a tsakanin al’umma.

Hukumar ta bayyana gamsuwa da matakan da gwamnati ke ɗauka wajen wadata ƙasa da abinci, amma ta yi gargaɗin cewa dole sai ta ƙara ƙaimi domin cim ma hakan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp