Home General Kungiyar likitoci ta baiwa gwamnan Kano awanni 48 ya kori Kwamishiniyar sa

Kungiyar likitoci ta baiwa gwamnan Kano awanni 48 ya kori Kwamishiniyar sa

Kungiyar likitoci ta baiwa gwamnan Kano awanni 48 ya kori Kwamishiniyar sa

Ƙungiyar Likitoci, NMA, reshen jihar Kano ta baiwa Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar wa’adin awanni 48 da ya kori Kwamishiniyar Jin-ƙai da Walwalar Al’umma, Amina Abdullahi bisa zargin cin zarafin wata likita to ta tafi yakin aiki.

A wata sanarwa da shugaban kungiyar, Dr Abdulrahman Ali da sakataren sa, Dr. Ibrahim D. Muhammad su ka fitar ta ce lamarin ya faru ne a ɓangaren yara na asibitin kwararru na Murtala Muhammad lokacin da likitar take duba marasa lafiya.

A cewar NMA, Kwamishiniyar ta je asibitin ne tare da tawogar ta, inda ta ci zarafin likitar saboda ta ce mata babu magungunan da Kwamishiniyar ta tambaya.

NMA ta kara da cewa a lokacin da lamarin ta faru, likitar ita kaɗai ce ke duba marasa lafiya sama da 100, “amma aka ci zarafin ta saboda wani abu da bata da iko a kai.”

“Hakan ya nuna yadda masu rike da mukamin siyasa ke ba zarar da ofishin su kuma ya nuna irin matsalar da ake da ita a fannin lafiya.

“Saboda haka mun bakwa gwamnan Kano awanni 48 da ya sallami Kwamishiniyar. In ba haka ba, to lamarin ba zai haifar da ɗa mai ido ba domin za mu janye aiyukan mu,”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp