Home General Kungiyar likitoci ta baiwa gwamnan Kano awanni 48 ya kori Kwamishiniyar sa

Kungiyar likitoci ta baiwa gwamnan Kano awanni 48 ya kori Kwamishiniyar sa

Kungiyar likitoci ta baiwa gwamnan Kano awanni 48 ya kori Kwamishiniyar sa

Ƙungiyar Likitoci, NMA, reshen jihar Kano ta baiwa Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar wa’adin awanni 48 da ya kori Kwamishiniyar Jin-ƙai da Walwalar Al’umma, Amina Abdullahi bisa zargin cin zarafin wata likita to ta tafi yakin aiki.

A wata sanarwa da shugaban kungiyar, Dr Abdulrahman Ali da sakataren sa, Dr. Ibrahim D. Muhammad su ka fitar ta ce lamarin ya faru ne a ɓangaren yara na asibitin kwararru na Murtala Muhammad lokacin da likitar take duba marasa lafiya.

A cewar NMA, Kwamishiniyar ta je asibitin ne tare da tawogar ta, inda ta ci zarafin likitar saboda ta ce mata babu magungunan da Kwamishiniyar ta tambaya.

NMA ta kara da cewa a lokacin da lamarin ta faru, likitar ita kaɗai ce ke duba marasa lafiya sama da 100, “amma aka ci zarafin ta saboda wani abu da bata da iko a kai.”

“Hakan ya nuna yadda masu rike da mukamin siyasa ke ba zarar da ofishin su kuma ya nuna irin matsalar da ake da ita a fannin lafiya.

“Saboda haka mun bakwa gwamnan Kano awanni 48 da ya sallami Kwamishiniyar. In ba haka ba, to lamarin ba zai haifar da ɗa mai ido ba domin za mu janye aiyukan mu,”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp