Home General Kungiyar likitoci ta baiwa gwamnan Kano awanni 48 ya kori Kwamishiniyar sa

Kungiyar likitoci ta baiwa gwamnan Kano awanni 48 ya kori Kwamishiniyar sa

Kungiyar likitoci ta baiwa gwamnan Kano awanni 48 ya kori Kwamishiniyar sa

Ƙungiyar Likitoci, NMA, reshen jihar Kano ta baiwa Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar wa’adin awanni 48 da ya kori Kwamishiniyar Jin-ƙai da Walwalar Al’umma, Amina Abdullahi bisa zargin cin zarafin wata likita to ta tafi yakin aiki.

A wata sanarwa da shugaban kungiyar, Dr Abdulrahman Ali da sakataren sa, Dr. Ibrahim D. Muhammad su ka fitar ta ce lamarin ya faru ne a ɓangaren yara na asibitin kwararru na Murtala Muhammad lokacin da likitar take duba marasa lafiya.

A cewar NMA, Kwamishiniyar ta je asibitin ne tare da tawogar ta, inda ta ci zarafin likitar saboda ta ce mata babu magungunan da Kwamishiniyar ta tambaya.

NMA ta kara da cewa a lokacin da lamarin ta faru, likitar ita kaɗai ce ke duba marasa lafiya sama da 100, “amma aka ci zarafin ta saboda wani abu da bata da iko a kai.”

“Hakan ya nuna yadda masu rike da mukamin siyasa ke ba zarar da ofishin su kuma ya nuna irin matsalar da ake da ita a fannin lafiya.

“Saboda haka mun bakwa gwamnan Kano awanni 48 da ya sallami Kwamishiniyar. In ba haka ba, to lamarin ba zai haifar da ɗa mai ido ba domin za mu janye aiyukan mu,”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp