Home General Likitocin Kano sun janye yajin aiki da suka tsunduma

Likitocin Kano sun janye yajin aiki da suka tsunduma

Kungiyar Likitoci na jihar Kano sun janye yajin aikin da suka fara a daren jiya, bayan Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusif ya sami nasarar sasanta rikicin dake faruwa, tsakanin kungiyar da kuma Kwamishiniyar Ma’aikatar Jin-kai ta jihar.

Shugaban Kungiyar Likitoci na jihar Kano Dakta Abdurrahman ne ya tabbatar da hakan, a yayin zantawar sa da manema Labaran a fadar Gwamnatin Kano.

Sanarwar da Kakakin Gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aiko wa jaridar PRNigeria ta kara da cewa, yanzu haka Likitocin sun koma bakin aiki domin ci-gaba da bawa marasa lafiya cikakkiyar kulawar da suka saba.

Dakta Abdurrahman ya ce sun janye yajin aikin ne bayan wani zama na musamman da Gwamnan Kano, akan sabanin da aka samu a tsakanin Mambar tasu da kuma ita waccan Kwamishiniya.

Ya kuma yaba wa Gwamnan a bisa gaggawar daukar matakin da ya kamata akan lamarin, harma yayi kira ga al’ummar jihar da su dinga bin dukkan hanyoyin da suka dace wajen shigar da korafin su akan jami’an lafiya domin a sami damar yin adalci ta hanyar bincika wa dama daukar matakin da ya kamata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp