Home General Sojojin Najeriya sun tabbatar da bullar sabuwar kungiyar ‘yan ta’adda a kasar

Sojojin Najeriya sun tabbatar da bullar sabuwar kungiyar ‘yan ta’adda a kasar

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da bullar wata sabuwar kungiyar ‘yan ta’adda a jihohin Sokoto da Kebbi da ake kira Lakurawas.

Mai magana da yawun rundunar Manjo Janar Edward Buba ya ce ‘yayan wannan sabuwar kungiyar sun fito ne daga kasashen Nijar da Mali, kuma ya zuwa yanzu ba’a iya sanin manufar kungiyar ba.

Buba yace wannan sabuwar kungiyar wadda ta bullo bayan juyin mulkin da akayi a Nijar, ta haifar da matsala a yakin da ake yi da ‘yan ta’adda a iyakokin Nijar da Najeriya.

Buba yace dakarun kasashen 2 na ci gaba da daukar mataki domin tabbatar da tsaro a kan iyakokon yankin.

Bullar wannan kungiyar ya dada tabbatar da karuwar matsalar tsaron da ake fuskanta a yankin arewa maso yammacin Najeriya da rikicin ‘yan bindiga ya daidaita wajen hallaka jama’a da kuma raba dubban mutane da garuruwansu, abinda ya kai ga wasu samun mafaka a Jamhuriyar Nijar.

Kakakin sojin ya ce a watan da ya gabata, dakarun Najeriya sun hallaka ‘yan ta’adda 163 tare da kama wasu 82 da kuma kubutar da akalla mutane 80 da akayi garkuwa da su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp