Home General Sojojin Najeriya sun tabbatar da bullar sabuwar kungiyar ‘yan ta’adda a kasar

Sojojin Najeriya sun tabbatar da bullar sabuwar kungiyar ‘yan ta’adda a kasar

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da bullar wata sabuwar kungiyar ‘yan ta’adda a jihohin Sokoto da Kebbi da ake kira Lakurawas.

Mai magana da yawun rundunar Manjo Janar Edward Buba ya ce ‘yayan wannan sabuwar kungiyar sun fito ne daga kasashen Nijar da Mali, kuma ya zuwa yanzu ba’a iya sanin manufar kungiyar ba.

Buba yace wannan sabuwar kungiyar wadda ta bullo bayan juyin mulkin da akayi a Nijar, ta haifar da matsala a yakin da ake yi da ‘yan ta’adda a iyakokin Nijar da Najeriya.

Buba yace dakarun kasashen 2 na ci gaba da daukar mataki domin tabbatar da tsaro a kan iyakokon yankin.

Bullar wannan kungiyar ya dada tabbatar da karuwar matsalar tsaron da ake fuskanta a yankin arewa maso yammacin Najeriya da rikicin ‘yan bindiga ya daidaita wajen hallaka jama’a da kuma raba dubban mutane da garuruwansu, abinda ya kai ga wasu samun mafaka a Jamhuriyar Nijar.

Kakakin sojin ya ce a watan da ya gabata, dakarun Najeriya sun hallaka ‘yan ta’adda 163 tare da kama wasu 82 da kuma kubutar da akalla mutane 80 da akayi garkuwa da su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp