Home Labarai Kotun koli ta yi watsi da ƙarar da ke kalubalantar dokar kafa...

Kotun koli ta yi watsi da ƙarar da ke kalubalantar dokar kafa EFCC

Kotun kolin Najeriya ta ƙori ƙarar da wasu manyan alkalai na jihohi suka shigar, inda suke kalubalantar dokar da ta kafa hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC.

Tawagar alkalai mai mambobi bakwai da alkali Uwani Abba Aji ta jagoranta, sun amince da ƙorar ƙarar saboda ba ta cancanci a saurare ta ba.

Ƙarar wadda alkalai na jihohi 16 suka shigar, na neman a rushe EFCC.

Yayin da wasu jihohi suka janye daga ƙarar, wasu sun ki yin haka inda suka ce za su kalubalanci lamarin.

Jihohin da suka shigar da ƙarar sun haɗa da Ondo da Edo da Oyo da Ogun da Nasarawa da Kebbi da Sokoto da Jigawa da Enugu da Benue da Anambra da Filato da Cross River da kuma Niger.

Sai dai a lokacin sauraron ƙarar ranar 22 ga watan Oktoba, jihohin Imo da Bauchi da kuma Osun su ma sun shiga cikin ƙarar yayin da Anambra da Ebonyi da kuma Adamawa suka sanar da janye wa daga ƙarar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp