Home Labarai Kotun koli ta yi watsi da ƙarar da ke kalubalantar dokar kafa...

Kotun koli ta yi watsi da ƙarar da ke kalubalantar dokar kafa EFCC

Kotun kolin Najeriya ta ƙori ƙarar da wasu manyan alkalai na jihohi suka shigar, inda suke kalubalantar dokar da ta kafa hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC.

Tawagar alkalai mai mambobi bakwai da alkali Uwani Abba Aji ta jagoranta, sun amince da ƙorar ƙarar saboda ba ta cancanci a saurare ta ba.

Ƙarar wadda alkalai na jihohi 16 suka shigar, na neman a rushe EFCC.

Yayin da wasu jihohi suka janye daga ƙarar, wasu sun ki yin haka inda suka ce za su kalubalanci lamarin.

Jihohin da suka shigar da ƙarar sun haɗa da Ondo da Edo da Oyo da Ogun da Nasarawa da Kebbi da Sokoto da Jigawa da Enugu da Benue da Anambra da Filato da Cross River da kuma Niger.

Sai dai a lokacin sauraron ƙarar ranar 22 ga watan Oktoba, jihohin Imo da Bauchi da kuma Osun su ma sun shiga cikin ƙarar yayin da Anambra da Ebonyi da kuma Adamawa suka sanar da janye wa daga ƙarar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp