Home General Majalisa ta sa a kamo Shugaban Kamfanin Julius Berger kan zargin N141bn

Majalisa ta sa a kamo Shugaban Kamfanin Julius Berger kan zargin N141bn

Majalisar Dattawa ta amince da ba da umarnin kamo mata Manajan Daraktan Kamfanin Gine-gine na Julius Berger, Mista Peer Lubasch.

Shugaban Majalisar, Sanata Godswill Akpabio ya ce ’yan majalisar sun ba da umarnin ne saboda sau uku Shugaban Kamfanin na kin amsa gayyatar majalisar.

Majalisar ta gayyaci shugaban kamfanin ne kan zargin ƙara Naira biliyan 141 a kuɗin aikin babban titin Itukpani zuwa Itu da ke jIhar Enugu, tare da yin watsi da aikin.

Da yake gabatar da ƙudurin, Mai Tsawatarwan Majalisa, Sanata Osita Ngwu, ya zargi kamfanin da ƙara kuɗin aikin daga Naira biliyan 54 zuwa biliyan 195.

Dan majalisar ta bayyana cewa daga bisani kamfanin ya kwashe kayansa daga wurin da ake aikin.

A kan haka ne sau uku majalisar ta na gayyatar shugaban kamfanin na Julius Berger ya zo ya yi bayani, amma ya yi watsi da su.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp