Home General Gwamnatin Nijeriya ta dakatar da Jirgi Max Air

Gwamnatin Nijeriya ta dakatar da Jirgi Max Air

Gwamnatin Najeriya ta hannun Hukumar kula da sufurin jragen sama ta ƙasar (NCAA) ta sanar da dakatar da ayyukan kamfanin jirgin sama na Max Air, bayan jirgin kamfanin ya yi hatsari a daren jiya Talata a jihar Kano.

Daraktan hulɗa da jama’a da kare haƙƙin abokan hulɗa na hukumar, Michael Achimugu – wanda ya fitar da sanarwar – ya ce dakatarwar za ta soma aiki ne a daren 31 ga watan Janairun 2025, domin bai wa hukumomin kamfanin damar tattance ayyukanta a cikin gida da ya haɗa da bincike kan kamfanin, ma’aikatansa, tsarin aikinsa da jiragensa, da kuma tattalin arziƙin kamfanin.

Achimugu ya kuma ce tuni hukumar tabbatar da kariya (NSIB) ta ƙaddamar da bincike kan musabbabin haɗarin na baya-bayan nan.

Jirgin Max Air samfurin B734 mai lambar rijista 5N-MBD, ya yi haɗari ne a yayin sauka a filin jirgin sama na Mallam Aminu Kano da ke Kano bayan tayarsa ta fashe a jiya Talata.

Duk da dai fasinjoji 53 da ke cikin jirgin sun fita lafiya, hukumar kula da filayen jiragen sama ta ƙasar (FAAN) ta rufe filin jirgin na wucin-gadi kafin buɗe shi a safiyar ranar Laraba.

Wannan ne karo na uku da ake samun haɗarin jirgin na Max Air a cikin wata uku.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp