Home General Majalisar dinkin Duniya ta zargi RSF da haifar da tarnaƙi a Sudan

Majalisar dinkin Duniya ta zargi RSF da haifar da tarnaƙi a Sudan

Majalisar Ɗinkin Duniya ta zargi mayaƙan rundunar RSF, da hana isar da kayan agaji yankin Darfur da ke fuskantar barazanar yunwa a Sudan da yaƙi ya ɗai-ɗaita.

A cikin wata sanarwa da jami’ar kula da ayyukan jin kai, ta Majalisar Ɗinkin Duniya da ke Sudan Clementine Nkweta-Salami ta fitar, ta ce wasu dokoki da RSF ta sanya a yankin na Darfur, na haifar da tarnaƙi wajen gudanar da ayyukan ceton rayukan jama’a.

Dakarun na RSF da ke fafata yaƙi da sojojin Sudan tun a watan Afrelun shekarar 2023, sun kasance masu rike da ikon yankin na Darfur, musammann yadda su ka mamaye birnin El-Fasher da ke Arewacinsa a watan Mayun shekarar da ta gabata.

An dai ayyana ɓarkewar yunwa a wasu yankuna biyar na Arewacin Darfur, kuma ana zaton ta ƙara bazuwa zuwa wasu yankuna biyar nan da watan Mayu mai zuwa.

A cewar wasu alkaluma da wata ƙungiya da ke samun goyon bayan Majalisar Ɗinkin Duniya ta fitar, sun nuna cewa kimanin mutum miliyan 7 ne ke fuskantar yunwa a yankin na Darfur.

A cewar wasu alkaluma da wata ƙungiya da ke samun goyon bayan Majalisar Ɗinkin Duniya ta fitar, sun nuna cewa kimanin mutum miliyan 7 ne ke fuskantar yunwa a yankin Darfur.

Majalisar Ɗinkin Duniya dai ta buƙaci RSF ta sauƙaƙa dokokin da ta sanya a yankin, don bada damar isar da kayan agaji ga al’ummar da ke cikin tsananin buƙata.

Shi dai yaƙin na Sudan ya lakume rayukan ɗaruruwan mutane, ya kuma raba sama da mutum miliyan 12 da muhallansu, sannan akwai wasu kimanin miliyan 25 da ke fuskantar barazanar yunwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp