Home General Majalisar dinkin Duniya ta zargi RSF da haifar da tarnaƙi a Sudan

Majalisar dinkin Duniya ta zargi RSF da haifar da tarnaƙi a Sudan

Majalisar Ɗinkin Duniya ta zargi mayaƙan rundunar RSF, da hana isar da kayan agaji yankin Darfur da ke fuskantar barazanar yunwa a Sudan da yaƙi ya ɗai-ɗaita.

A cikin wata sanarwa da jami’ar kula da ayyukan jin kai, ta Majalisar Ɗinkin Duniya da ke Sudan Clementine Nkweta-Salami ta fitar, ta ce wasu dokoki da RSF ta sanya a yankin na Darfur, na haifar da tarnaƙi wajen gudanar da ayyukan ceton rayukan jama’a.

Dakarun na RSF da ke fafata yaƙi da sojojin Sudan tun a watan Afrelun shekarar 2023, sun kasance masu rike da ikon yankin na Darfur, musammann yadda su ka mamaye birnin El-Fasher da ke Arewacinsa a watan Mayun shekarar da ta gabata.

An dai ayyana ɓarkewar yunwa a wasu yankuna biyar na Arewacin Darfur, kuma ana zaton ta ƙara bazuwa zuwa wasu yankuna biyar nan da watan Mayu mai zuwa.

A cewar wasu alkaluma da wata ƙungiya da ke samun goyon bayan Majalisar Ɗinkin Duniya ta fitar, sun nuna cewa kimanin mutum miliyan 7 ne ke fuskantar yunwa a yankin na Darfur.

A cewar wasu alkaluma da wata ƙungiya da ke samun goyon bayan Majalisar Ɗinkin Duniya ta fitar, sun nuna cewa kimanin mutum miliyan 7 ne ke fuskantar yunwa a yankin Darfur.

Majalisar Ɗinkin Duniya dai ta buƙaci RSF ta sauƙaƙa dokokin da ta sanya a yankin, don bada damar isar da kayan agaji ga al’ummar da ke cikin tsananin buƙata.

Shi dai yaƙin na Sudan ya lakume rayukan ɗaruruwan mutane, ya kuma raba sama da mutum miliyan 12 da muhallansu, sannan akwai wasu kimanin miliyan 25 da ke fuskantar barazanar yunwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp