Home General Najeriya da Nijar da kuma Aljeriya sun cimma yarjejeniyar shimfiɗa bututun gas...

Najeriya da Nijar da kuma Aljeriya sun cimma yarjejeniyar shimfiɗa bututun gas zuwa Turai

Ƙasashen Aljeriya da Najeriya da kuma Jamhuriyar Nijar, sun ƙulla sabuwar yarjejeniya da nufin gaggauta gudanar da akin shimfiɗa bututun iskar gas mai tsawon kilomita sama da dubu 4, da zai sada ƙasashen da nahiyar Turai.

A yarjejeniyar, ƙasashen 3 sun amince su yi amfani da bututun Transmed wanda Aljeriya ke amfani da shi don bai wa Italiya makamashin gas, sai a yanzu maimakon Italiya kawai da ke cin gajiyarsa, za a riƙa tura makamashin zuwa sauran ƙasashen Turai.

Yarjejeniyar da wakilan ƙasashen uku suka rattaba wa hannu ranar Talata da ta gabata, ta fayyace adadin kuɗaɗe da tsawon lokacin da ake buƙata don aiwatar da wannan aikin, sai kuma batun biyan diyya da kuma zaɓen ƙmfanonin da za su aiwatar da wannan aiki.

Tun a shekara ta 2009 ne ƙasashen 3 suka tattaunawa domin shimfiɗa wannan bututu mai tsawo kilomita dubu 4 da 128, kuma tun a wancan lokaci an kiyasta cewa ana bukatar Dala bilyan 10 domin aiwatar da aikin.

Rikicin Rasha da Ukraine ne ya ƙara zaburar da waɗannan ƙasashe domin gaggauta aiwatar da wannan aiki na bututun iskar gas, musamman lura da cewa tun a 2022 mafi yawan ƙasashen Turai sun bayyana aniyarsu ta daina dogara da Rasha domin samun makamashin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp