Home General Najeriya da Nijar da kuma Aljeriya sun cimma yarjejeniyar shimfiɗa bututun gas...

Najeriya da Nijar da kuma Aljeriya sun cimma yarjejeniyar shimfiɗa bututun gas zuwa Turai

Ƙasashen Aljeriya da Najeriya da kuma Jamhuriyar Nijar, sun ƙulla sabuwar yarjejeniya da nufin gaggauta gudanar da akin shimfiɗa bututun iskar gas mai tsawon kilomita sama da dubu 4, da zai sada ƙasashen da nahiyar Turai.

A yarjejeniyar, ƙasashen 3 sun amince su yi amfani da bututun Transmed wanda Aljeriya ke amfani da shi don bai wa Italiya makamashin gas, sai a yanzu maimakon Italiya kawai da ke cin gajiyarsa, za a riƙa tura makamashin zuwa sauran ƙasashen Turai.

Yarjejeniyar da wakilan ƙasashen uku suka rattaba wa hannu ranar Talata da ta gabata, ta fayyace adadin kuɗaɗe da tsawon lokacin da ake buƙata don aiwatar da wannan aikin, sai kuma batun biyan diyya da kuma zaɓen ƙmfanonin da za su aiwatar da wannan aiki.

Tun a shekara ta 2009 ne ƙasashen 3 suka tattaunawa domin shimfiɗa wannan bututu mai tsawo kilomita dubu 4 da 128, kuma tun a wancan lokaci an kiyasta cewa ana bukatar Dala bilyan 10 domin aiwatar da aikin.

Rikicin Rasha da Ukraine ne ya ƙara zaburar da waɗannan ƙasashe domin gaggauta aiwatar da wannan aiki na bututun iskar gas, musamman lura da cewa tun a 2022 mafi yawan ƙasashen Turai sun bayyana aniyarsu ta daina dogara da Rasha domin samun makamashin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp