Home General Kotun Ƙoli ta amince da ɓangaren Wike na majalisar jihar Rivers

Kotun Ƙoli ta amince da ɓangaren Wike na majalisar jihar Rivers

Kotun Ƙolin Najeriya ta umarci babban akanta da babban bankin ƙasar wato CBN na Najeriya da su dakatar da kason kuɗin jihar Rivers, har sai gwamnan jihar ya gabatar da kasafin kuɗin a gaban halastacciyar majalisar jihar.

Alƙalan kotun su biyar ne suka yanke wannan hukuncin, inda kotun ta ce Martins Amaewhule ne sahihin shugaban majajlisar.

Wannan ya kawo ƙarshen lokaci mai tsawo da aka ɗauka ana shari’a tsakanin ɓangarorin biyu kan rikita-rikitar siyasa a jihar.

Haka kuma ana ganin wannan matakin a matsayin wata nasara ga ɓangaren Ministan Abuja, Nyesome Wike, kan Gwamnan jihar, Sim Fubara.

Mai shari’a Emmanuel Agim ne ya karanta hukuncin, inda ya ce, “muna umartar Babban Bankin Najeriya CBN da Babban Akanta na Najeriya da su dakata da tura kuɗin kason jihar Rivers har sai gwamnan ya gabatar da kasafin kuɗin a gaban majalisar jihar ƙarƙashin Martin Amaewhule,” kamar yadda ya bayyana.

A gefe guda kuma, a wata shari’ar daban, kotun ƙolin ta soke zaɓen ƙananan hukumomin jihar da aka yi a ranar 5 ga Oktoban 2024.

Mai shari’a Jamilu Tukur, ya ce zaɓen wanda hukumar zaɓen Rivers mai zaman kanta ta shirya, ya saɓa da sashe na 150 na kundin tsarin zaɓe na ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp