Home General Za mu hukunta Jami’anmu dake karbar kudi a hannun dan Chana

Za mu hukunta Jami’anmu dake karbar kudi a hannun dan Chana

Rundunar ƴansandan Najeriya ta ce za ta hukunta jami’anta da aka nuna suna ƙarbar kuɗaɗe daga hannun wasu ƴan ƙasar China a wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta.

A cikin bidiyon, an ga wasu ƴan ƙasar China suna rabawa wasu jerin jami’an ƴansanda kuɗi, lamarin dai ya janyo ce-ce-ku-ce a shafukan sada zumunta, inda ƴan Najeriya da dama ke nuna rashin jin daɗinsu tare da yin kira da a kawo sauyi kan yadda rundunar ke gundanar da ayyukanta.

A wata sanarwa da aka wallafa a shafin rundunar ƴansandan na dandalin X, kakakin rundunar Muyiwa Adejobi, ya yi Allah-wadai da halin jami’an, inda ya bayyana abin da suka yi a matsayin rashin da’a.

Ya ce, “Halayyar waɗannan jami’an ta saɓawa ƙa’idojin da’a, da muhimman dabi’u na rundunar ƴansandan Najeriya.”

Ya ƙara da cewa rundunar ta zuƙulo jami’an da lamarin ya shafa kuma ana shirin ɗaukar matakan ladabtarwa a kansu.

Ko da yake bai bayyana yanayin matakan da za a ɗauka kan ƴansanda ba, Adejobi ya tabbatar wa jama’a cewa za a yi adalci.

Rundunar ta kuma gargadi mutane da ƙungiyoyi masu amfani da ƴansanda, a matsayin masu rakiya da masu gadi da su kaucewa duk wani aiki da zai iya zubar da mutuncin jami’anta ko kuma janyo wa rundunar bacin suna.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp