Home General Za mu hukunta Jami’anmu dake karbar kudi a hannun dan Chana

Za mu hukunta Jami’anmu dake karbar kudi a hannun dan Chana

Rundunar ƴansandan Najeriya ta ce za ta hukunta jami’anta da aka nuna suna ƙarbar kuɗaɗe daga hannun wasu ƴan ƙasar China a wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta.

A cikin bidiyon, an ga wasu ƴan ƙasar China suna rabawa wasu jerin jami’an ƴansanda kuɗi, lamarin dai ya janyo ce-ce-ku-ce a shafukan sada zumunta, inda ƴan Najeriya da dama ke nuna rashin jin daɗinsu tare da yin kira da a kawo sauyi kan yadda rundunar ke gundanar da ayyukanta.

A wata sanarwa da aka wallafa a shafin rundunar ƴansandan na dandalin X, kakakin rundunar Muyiwa Adejobi, ya yi Allah-wadai da halin jami’an, inda ya bayyana abin da suka yi a matsayin rashin da’a.

Ya ce, “Halayyar waɗannan jami’an ta saɓawa ƙa’idojin da’a, da muhimman dabi’u na rundunar ƴansandan Najeriya.”

Ya ƙara da cewa rundunar ta zuƙulo jami’an da lamarin ya shafa kuma ana shirin ɗaukar matakan ladabtarwa a kansu.

Ko da yake bai bayyana yanayin matakan da za a ɗauka kan ƴansanda ba, Adejobi ya tabbatar wa jama’a cewa za a yi adalci.

Rundunar ta kuma gargadi mutane da ƙungiyoyi masu amfani da ƴansanda, a matsayin masu rakiya da masu gadi da su kaucewa duk wani aiki da zai iya zubar da mutuncin jami’anta ko kuma janyo wa rundunar bacin suna.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp