Home General Dakta Abubakar Tanko Bala ya zama sabon shugaban Shirin nan na...

Dakta Abubakar Tanko Bala ya zama sabon shugaban Shirin nan na “Gas-by-Rail Freight Corridors Initiative” a Nijeriya

Sabon Ko-odinatan shirin nan Shirin nan “Gas-by-Rail Freight Corridors Initiative” na Najeriya, Dakta Abubakar Tanko Bala, ya yi alkawarin yin amfani da sabon mukamin nasa wajen ciyar da Najeriya gaba.

Dakta Abubakar ya bayyana hakan ne jim kadan da amsar takardar nadin mukamin nasa, wadda babban jami’in dake kula da shirin a fadin Duniya, Ambasada Musa Ibrahim Kuchi, ya sanya wa hannu, har kuma aka turawa Ko-odinatan shirin na Afirka ta yamma, Kabir Ishaq Sa’id Kwafin ta.

Dakta Tanko dai zai jagoranci masu ruwa da tsakin shirin a fadin Najeriya, wanda yake hadin gwiwa da ofishin majalisar dinkin Duniya, (United Nations Global Compact da Insight Dynamic Resources Ltd).

Manufar shirin shine domin samar da titin jirgin kasa me girman Kilo Mita dubu 70 a tsakanin kasashe 40 na Sahara dake nahiyar Afirka daga nan zuwa shekarar 2035, ta yadda zai bada damar taimaka wa al’umma wajen inganta harkokin sufuri da cinikayya a yankin Sahara na nahiyar Afirka

Haka kuma zai taka rawa wajen bunkasa tattalin arzikin, kare muhalli, inganta harkokin sufuri, la’akari da yadda za’a samar da guraben aiyukan yi kimanin Milyan 170 daga nan zuwa shekarar 2050.

A karshe ya buƙaci al’ummar kasar su taya shi da addu’ar Allah ya bashi ikon kawo canji mai ma’ana, ta yadda zai bada tasa gudunmawar wajen samar da kyakykyawar makoma ga kasar dama mutanen ta gaba-daya.

Dakta Abubakar Tanko Bala, dai ya kasance Sakatare Janar na Cibiyar nan ta shirya gasa a nahiyar Afirka, (Pan African Competitibeness Forum (PACF) reshen Najeriya, haka kuma shine ma’ajin kungiyar masu kanana da matsakaitan masana’antu na (NASSI) na Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp