Home General Dakta Abubakar Tanko Bala ya zama sabon shugaban Shirin nan na...

Dakta Abubakar Tanko Bala ya zama sabon shugaban Shirin nan na “Gas-by-Rail Freight Corridors Initiative” a Nijeriya

Sabon Ko-odinatan shirin nan Shirin nan “Gas-by-Rail Freight Corridors Initiative” na Najeriya, Dakta Abubakar Tanko Bala, ya yi alkawarin yin amfani da sabon mukamin nasa wajen ciyar da Najeriya gaba.

Dakta Abubakar ya bayyana hakan ne jim kadan da amsar takardar nadin mukamin nasa, wadda babban jami’in dake kula da shirin a fadin Duniya, Ambasada Musa Ibrahim Kuchi, ya sanya wa hannu, har kuma aka turawa Ko-odinatan shirin na Afirka ta yamma, Kabir Ishaq Sa’id Kwafin ta.

Dakta Tanko dai zai jagoranci masu ruwa da tsakin shirin a fadin Najeriya, wanda yake hadin gwiwa da ofishin majalisar dinkin Duniya, (United Nations Global Compact da Insight Dynamic Resources Ltd).

Manufar shirin shine domin samar da titin jirgin kasa me girman Kilo Mita dubu 70 a tsakanin kasashe 40 na Sahara dake nahiyar Afirka daga nan zuwa shekarar 2035, ta yadda zai bada damar taimaka wa al’umma wajen inganta harkokin sufuri da cinikayya a yankin Sahara na nahiyar Afirka

Haka kuma zai taka rawa wajen bunkasa tattalin arzikin, kare muhalli, inganta harkokin sufuri, la’akari da yadda za’a samar da guraben aiyukan yi kimanin Milyan 170 daga nan zuwa shekarar 2050.

A karshe ya buƙaci al’ummar kasar su taya shi da addu’ar Allah ya bashi ikon kawo canji mai ma’ana, ta yadda zai bada tasa gudunmawar wajen samar da kyakykyawar makoma ga kasar dama mutanen ta gaba-daya.

Dakta Abubakar Tanko Bala, dai ya kasance Sakatare Janar na Cibiyar nan ta shirya gasa a nahiyar Afirka, (Pan African Competitibeness Forum (PACF) reshen Najeriya, haka kuma shine ma’ajin kungiyar masu kanana da matsakaitan masana’antu na (NASSI) na Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp