Home General Najeriya na fuskantar tsaiko kan shirinta na karɓar Dala biliyan 5 daga...

Najeriya na fuskantar tsaiko kan shirinta na karɓar Dala biliyan 5 daga Saudiya

Wani rahoton Kamfanin Dillancin Labarai na Reuters ya ce ana fuskantar tsaiko a tattaunawar da ake yi tsakanin Najeriya da kamfanin man fetur mafi girma a duniya mallakin Saudiya wato Aramco, dangane da shirin karɓar rancen Dala biliyan 5 da Najeriyar za ta biya da ɗanyen manta.

Wasu majiyoyi huɗu sun shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa faɗuwar baya bayan nan da farashin ɗanyen mai yayi a kasuwannin duniya shi ne ya janyo tsaikon, bayan da bankunan da ake sa ran za su taimaka wajen aiwatar da yarjejeniyar suka bayyana damuwa kan sauyin farashin da aka samu.

Wasu alƙaluma dai sun nuna faɗuwar farashin ɗanyen mai nau’in Brent da kashi 20 cikin 100, inda ya koma Dala 65 daga Dala 82 a cikin watan Janairun da ya gabata, abinda ke nufin idan har ba za a fasa ƙulla yarjejeniyar karɓar rancen na Dala biliyan 5 ɗin ba, to fa dole Najeriya ta ƙara yawan gungunan ɗanyen man da za ta yi amfani da su wajen biyan bashin.

Biyu daga cikin majiyoyin da suka zanta Reuters, sun ce an fara tattaunawa kan shirin karɓar rancen ne a watan Nuwamban da ya gabata, lokacin da shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gana da Yarima mai jiran gadon Sarautar  Saudiya Muhd Bin salman a yayin taron tattalin arziƙin da aka yi tsakanin Saudiyan da ƙasashen Afrika. Sai dai tun babu wani ƙarin bayani da aka taɓa bayyanawa kan neman bashin da Najeriyar ke yi, in banda yanzu da kamfanin dillancin labarai na Reuters da ya ruwaito.

Idan za a iya tunawa cikin watan Mayu, shugaba Tinubu ya nemi amincewar ‘yan Majlisar ƙasar kan buƙatar gwamnati ta karɓo bashin Dala biliyan 21 daga ƙasashen ƙetare, wanda kuma a ciki ne Najeriyar ke neman rancen na dala biliyan 5 daga kamfanin Man Saudiya na Aramco.

Ya zuwa yanzu dai kamfanin dillancin labarai na Reuters bai gano manyan bankunan da za su taimaka wajen aiwatar da wannan yarjejeniya ba, sai dai majiyoyinsa sun shaida masa cewar akwai guda daga nahiyar Afrika, yayin da ragowar za su kasance daga Yankin Gabas ta Tsakiya.

Idan har wannan yarjejeniyar karɓar bashin ta ƙullu, za ta kasance mafi girma irinta da Najeriya ta shiga, kuma karo na farko kenan da irin hulɗar ke shiga tsakanin Najeriyar da Saudiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp