Home General Tinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyya

Tinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyya

Bola Ahned Tinubu

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu zai yi jawabi ga al’ummar ƙasar da misalin ƙarfe 7 na safe a ranar Alhamis domin bikin ranar Dimokuraɗiyya ta shekarar 2025.

Cikin wata sanarwa da kwamitin shirya bikin ranar Dimokradiyyar ya fitar, ya ce da rana kuma Tinubu zai halarci zaman haɗin gwiwa da ƴan majalisar dokokin ƙasar.

Sai dai sanarwar ta bayyana cewa ba za a gudanar da taron faretin ranar ba a bana. A maimakon haka, za a gudanar da muhawarar jama’a a ɗakin taro na fadar shugaban ƙasa da ƙarfe 4 na yamma.

Bikin na bana na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasar ke cika shekara 26 ƙarƙashin mulkin dimokradiyya ba tare da katsewa ba tun bayan kawo ƙarshen mulkin soja a 1999.

A baya ana bikin ranar dimokradiyya a ranar 29 ga Mayu, wadda ke zama ranar rantsar da shugabannin ƙasa da gwamnoni da kuma ƴan majalisar tarayya da na jihohi.

Amma daga shekarar 2018, an sauya ranar zuwa 12 ga Yuni domin girmama zaɓukan 1993 da aka soke – da MKO Abiola ya lashe – zaɓen da ake ganin mafi sahihanci a tarihin Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp