Home General DR Congo da Rwanda sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya

DR Congo da Rwanda sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya

Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo (DRC) da ƙasar Rwanda sun amince da yarjejeniyar zaman lafiya da nufin kawo ƙarshen rikicin da ke ci gaba da ɗaukar hankula a gabashin DRC, wanda ke da arzikin ma’adinai.

Ministocin harkokin wajen ƙasashen biyu ne za su rattaba hannu a yarjejeniyar wadda Amurka ta shiga tsakani don warware rikicin, a mako mai zuwa, ranar 27 ga Yuni.

Yarjejeniyar na da nufin a ƙwace makaman mayaƙa, da kuma dawo da damar agajin jin ƙai ga al’umma a yankin da rikicin ya addaba.

Yarjejeniyar ta ƙunshi sharuɗɗa masu muhimmanci kamar girmama cikakken ikon ƙasa da iyakokin juna da haramta ci gaba da faɗa da Janyewar mayaƙa daga yankunan da suka mamaye da ƙwace makamai da kuma taimakawa wajen dawo da ‘yan gudun hijira da waɗanda rikicin ya raba da muhallansu

Tun farkon shekarar nan ne mayaƙan M23 suka ƙwace manyan birane biyu mafi muhimmanci a gabashin DR Congo.

DR Congo ta zargi Rwanda da bayar da tallafi da makamai ga mayaƙan, amma Rwanda ta musanta hakan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp