Home General DR Congo da Rwanda sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya

DR Congo da Rwanda sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya

Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo (DRC) da ƙasar Rwanda sun amince da yarjejeniyar zaman lafiya da nufin kawo ƙarshen rikicin da ke ci gaba da ɗaukar hankula a gabashin DRC, wanda ke da arzikin ma’adinai.

Ministocin harkokin wajen ƙasashen biyu ne za su rattaba hannu a yarjejeniyar wadda Amurka ta shiga tsakani don warware rikicin, a mako mai zuwa, ranar 27 ga Yuni.

Yarjejeniyar na da nufin a ƙwace makaman mayaƙa, da kuma dawo da damar agajin jin ƙai ga al’umma a yankin da rikicin ya addaba.

Yarjejeniyar ta ƙunshi sharuɗɗa masu muhimmanci kamar girmama cikakken ikon ƙasa da iyakokin juna da haramta ci gaba da faɗa da Janyewar mayaƙa daga yankunan da suka mamaye da ƙwace makamai da kuma taimakawa wajen dawo da ‘yan gudun hijira da waɗanda rikicin ya raba da muhallansu

Tun farkon shekarar nan ne mayaƙan M23 suka ƙwace manyan birane biyu mafi muhimmanci a gabashin DR Congo.

DR Congo ta zargi Rwanda da bayar da tallafi da makamai ga mayaƙan, amma Rwanda ta musanta hakan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp