Home Labarai Sojojin Najeriya sun kashe ƴan Bindiga fiye da 100 a jihar Neja

Sojojin Najeriya sun kashe ƴan Bindiga fiye da 100 a jihar Neja

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta tare da haɗin gwiwar ƴan sa-kai waɗanda ake kira bijilanti sun samu nasarar hallaka ‘yan bindiga biyo bayan wata fafatawa da suka yi  a tsakaninsu a ƙauyen Warari da ke Jihar Neja.

Rundunar ta ce artabun dai ya faru ne a ranar Talata wanda ta sami nasarar hallakafiye da ‘yan bindiga 100 waɗanda ke gilmawa a kan babura.

Lamarin ya faru ne bayan wani bayanin sirri da dakrun suka samu daga mazauna yankin game da hanyoyin da ‘yan bindiga ke bi don satar shanu.

Wannan ne ya bai wa sojojin damar kitsa kwanton-ɓauna da ya kai ga fafatawar da ta kai ga hallaka ƴan bindigan da dama.

wata shaidu sun tabbatarwa da PRNigeria cewa sojojin sun yi amfani da motoci masu sulke da makamai na zamani wanda ya ba su galaba a kan ‘yan bindigar.

Shugabannin al’umma a Warari sun tabbatar da girman rashin da ‘yan bindigar suka tafka, inda suka bayyana cewa gawarwakin wasu daga cikin su sun bazu a tituna da gonaki da dazuka da ke kewaye da yankin.

Neja na cikin jihohin Najeriya da ke fama da hare-haren ƴan bindiga masu kisa da kuma garkuwa da mutane domin neman kudin fansa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp