Home Labarai An samu gagarumar raguwar matsalar tsaro a Zamfara – Sojoji

An samu gagarumar raguwar matsalar tsaro a Zamfara – Sojoji

Babban kwamandan runduna da ɗaya ta sojin Najeriya da ke Gusau, Birgediya Janar Mustapha Jimoh, ya ce ayyukan ƴanbindiga da ƴanta’adda a jihar Zamfara sun yi matuƙar raguwa.

Yayin da yake jawabi ga manema labarai a wani taro na musamman da rundunar ta shirya a birnin Gusau, Janar Jimoh ya ce hare-haren soji a jihar ƙarƙashin rundunar Fansan Yamma sun yi matuƙar inganta tsaro da zaman lafiya a jihar, kamar yadda gidan talbijin na Channels ya ruwaito.

Janar Jimo ya ƙara da cewa matakin ya sa a yanzu mazauna jihar da matafiya za su yi tafiye-tafiyensu cikin kwanciyar hankali ba tare da fargabar hare-haren ƴanbindiga ba.

“Za ku iya zama shaida a yanzu za ku iya yin tafiya daga Funtua zuwa Gusau, ko Gusau zuwa Sokoto ba tare da wata fargaba ba, don haka za mu iya cewa an samu gagarumar raguwar matsalar tsaro a jihar Zamfara”, in ji shi.

Kwamandan rundunar sojin ya ce rundunarsa za ta ci gaba da ƙoƙari wajen kakkaɓe ragowar ayyukan ƴanbindigar ba a Zamfara kawai ba, har ma da sauran jihohin arewa maso yammacin Najeriya da ma ƙasar baki ɗaya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp