Home Labarai An samu gagarumar raguwar matsalar tsaro a Zamfara – Sojoji

An samu gagarumar raguwar matsalar tsaro a Zamfara – Sojoji

Babban kwamandan runduna da ɗaya ta sojin Najeriya da ke Gusau, Birgediya Janar Mustapha Jimoh, ya ce ayyukan ƴanbindiga da ƴanta’adda a jihar Zamfara sun yi matuƙar raguwa.

Yayin da yake jawabi ga manema labarai a wani taro na musamman da rundunar ta shirya a birnin Gusau, Janar Jimoh ya ce hare-haren soji a jihar ƙarƙashin rundunar Fansan Yamma sun yi matuƙar inganta tsaro da zaman lafiya a jihar, kamar yadda gidan talbijin na Channels ya ruwaito.

Janar Jimo ya ƙara da cewa matakin ya sa a yanzu mazauna jihar da matafiya za su yi tafiye-tafiyensu cikin kwanciyar hankali ba tare da fargabar hare-haren ƴanbindiga ba.

“Za ku iya zama shaida a yanzu za ku iya yin tafiya daga Funtua zuwa Gusau, ko Gusau zuwa Sokoto ba tare da wata fargaba ba, don haka za mu iya cewa an samu gagarumar raguwar matsalar tsaro a jihar Zamfara”, in ji shi.

Kwamandan rundunar sojin ya ce rundunarsa za ta ci gaba da ƙoƙari wajen kakkaɓe ragowar ayyukan ƴanbindigar ba a Zamfara kawai ba, har ma da sauran jihohin arewa maso yammacin Najeriya da ma ƙasar baki ɗaya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp