Home Labarai ITU Ta nada Pantami Matsayin Jagora a Taron ta na Duniya a...

ITU Ta nada Pantami Matsayin Jagora a Taron ta na Duniya a kasar Switzerland

Kungiyar Sadarwa ta Kasa da Kasa wato International Telecommunication Union (ITU) ta nada Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, a matsayin shugaban taron kolin kingiyar da gudana a shalkwatar kungiyar dake Geneva a kasar Switzerland.

Kungiyar Ta ITU ta tabbatar da nadin na Pantami ta cikin wata wasika mai dauke da sa hannun babban sakatern ta, wanda ya bayyana cewa kungiyar ta nada Farfesa Pantami matsayin shugaban taron kolin ta.

”Bisa la’akari da sadaukarwarsa ga kungiya, da kuma rawar da yake takawa a cikin tsare tsaren gudanar da taron na WSIS” masu ruwa da tsaki sunga dacewar nadashi bisa wannan matsayi, taron zai sami halartar manyan ministoci daga kasashen dake cikin wannan kungiya.

Dandalin taron na WSIS 2022 na matsayin babban dandalin tattaunawa gami da rawar da hanyoyin sadarwa ke takawa, kuma tana matsayin hanyar aiwatar da manufofin cigaba mai dorewa, bisa la’akari da tsarin da duniya ke kai gami da bibiyar hanyoyin aiwatar da kudirin cigaba mai dorewa zuwa shekarar 2030 na (UNGA Resolution A/&70/1).

Haka zalika dandamalin na WSIS na bin diddigin nasarorin da ake samu bisa hadin Gwiwar hukumomin Majalisar Dinkin Duniya da abin ya shafa, ta hanayar samar da bayanan binciken da suka gudanar.

Taron na WSIS, na kungiyar ITU da asusun tallafawa kananan yar ana majalisar dinkin duniyar da UNCTAD suka shirya tare da hadin wasu hukumomin majalisar dinkin duniyar guda 24, da suka hadar da FAO, ILO, ITC, UNDESA, UNICO, UNITAR, UNHCR, UNODC, UNEP, UPU, UN TECH BANK, WMO, WIPO, WHO, WFP da dai sauransu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp