Home Labarai ‘Yan Bindiga Sun Raunata Magidanci Tare Da Yin Awon Gaba Da ‘Dan...

‘Yan Bindiga Sun Raunata Magidanci Tare Da Yin Awon Gaba Da ‘Dan Sa A Abuja

Wasu mahara da ake zargin ‘Yan Bindiga ne sun yi awon gaba da wani matashi mai kimanin shekaru 18 da haihuwa mai suna Victor Egbon a unguwar Zone A dake yankin Kuje a birnin tarayya Abuja, bayan sun raunata mahaifinsa.

Victor da ne ga mamallakin makarantar Supreme Kids Academy, dake birnin tarayyar Nijeriya.

An rawaito cewa an garzaya da mahaifin matashin mai suna Abdulsalam Ozigi asibiti sakamakon mugun raunin da ‘yan ta’addar suka ji masa a jikin shi.

Wani shaidar gani da ido da ya nemi a sakayi sunan sa, yace ‘yan bindigar sun kai farmaki gidan Ozigi da misalin karfe 12:15 na daren litinin, inda suka yi awon gaba da Victor bayan sun lalata wasu kofofin gidan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp