Home Labarai Rundunar Farar Hula ta Kashe ‘Yan Bindiga 9, ta Kama 5 a...

Rundunar Farar Hula ta Kashe ‘Yan Bindiga 9, ta Kama 5 a Katsina

Rundunar Farar Hula ta Kashe ‘Yan Bindiga 9, ta Kama 5 a Katsina

 

A ranar Lahadin da ta gabata ne ‘yan kungiyar Civilian Joint Task Force suka dakile wani hari da suka kai wani gari a karamar hukumar Batsari ta jihar Katsina tare da kashe wasu ‘yan ta’adda biyu.

Rundunar ‘yan sandan ta kuma cafke wasu ‘yan ta’adda biyar tare da kame babura tara da aka yi amfani da su wajen kai harin.

Wasu majiyoyi da suka zanta da wakilinmu sun ce ‘yan ta’addan sun kai hari garin ne da misalin karfe 4:30 na yamma, inda suka ce ‘yan ta’addan sun mamaye garin ne a cikin babura akalla 10.

A yayin farmakin, tawagar da ke yaki da ‘yan ta’addan sun yi arangama da ‘yan ta’addan, kuma a yayin musayar wuta da bindiga, sun kashe mutane tara da ake zargi.

Rahotanni sun bayyana cewa rundunar ta kama wasu ‘yan kungiyar su biyar a yayin samamen.

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Gambo Isah, ya ce har yanzu DPO da ke yankin bai yi wa rundunar bayanin faruwar lamarin ba.

Isah ya ce, “Zan yi muku bayani a duk lokacin da DPO na yankin ya sanar da hukumar game da lamarin.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp