Home Labarai Kungiyar CAN ta yi Allah-wadai da yunkurin kashe mai taimaka wa Gwamnan...

Kungiyar CAN ta yi Allah-wadai da yunkurin kashe mai taimaka wa Gwamnan Bauchi

Bala mohammed

Kungiyar CAN ta yi Allah-wadai da yunkurin kashe mai taimaka wa Gwamnan Bauchi

 

AREWA AGENDA – Kungiyar kiristoci ta Najeriya reshen jihar Bauchi CAN ta yi Allah wadai da yunkurin wasu ‘yan bindiga da har yanzu ba a san ko su wanene ba na yunkurin kashe babban mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Bauchi kan harkokin addinin Kirista Fasto Zakka Magaji.

Shugaban kungiyar CAN reshen Bauchi, Rabaran Dr Abraham Damina Dimeus ya bayyana haka a lokacin da ya jagoranci jami’an kungiyar a ziyarar jaje a gidan hadimin gwamnan da ke Birshi, al’ummar da ke wajen birnin Bauchi.

Ya ce harin ba abin da ya dace ba kuma abin takaici ne, yana mai cewa ya kamata mutane su sani cewa rayuwa abu ne mai tsarki kuma dole ne a kiyaye ta ko ta halin kaka.

Shugaban kungiyar ta CAN wanda ya yi godiya ga Allah da cewa ba a samu asarar rai ba yayin harin kamar yadda ba a yi garkuwa da kowa ba, ya jaddada bukatar karfafa tsaro a fadin kasar nan.

Ya kuma yi kira ga hukumomin tsaro da abin ya shafa musamman a jihar da ma kasar baki daya da su gaggauta daukar matakan tsaro musamman a yankunan da ke fuskantar hare-haren ‘yan bindiga.

Da yake yabawa gwamnatin jihar karkashin jagorancin gwamnan jihar Sen Bala Mohammed Abdulkadir bisa kokarin da take yi na kare rayuka da dukiyoyin mazauna jihar, ya ce za a iya kara kaimi kan lamarin.

Abraham Damina ya kuma yi kira ga al’umma da su kasance masu lura da tsaro da kuma sa kai wajen bada bayanai game da miyagun qwai a cikin al’umma domin a ci gaba da samun zaman lafiya a jihar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp