Home Labarai Maulid: Ministan Tsaron Nijeriya Ya bukaci Addu’oi Domin Magance Rashin Tsaro

Maulid: Ministan Tsaron Nijeriya Ya bukaci Addu’oi Domin Magance Rashin Tsaro

Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta bukaci Al’ummar musulmi dasu yi amfani da lokacin bukukuwan maulidu wajen yiwa kasar Addu’ar kan matsalolin tsaron da suka addabi Al’ummar ta.

Wannna na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mataimaki na musamman ga Ministan tsaron Nijeriya Manjo Janar Bashir Salihi Magashi mai ritaya, kan harkokin sadarwa Mohammad Abdulkadri ya fitar domin taya Al’ummar Musulmi murnar Mauludin Fiyayyen Halitta na bana.

Yace haihuwar fiyayyen halitta ta zo wa da duniya da abubuwan da suka jibanci yadda za’ayi koyi da hakuri, addu’oi da Kankan da kai, gami da tsoron Allah, wadanda a cewar sa sun cancanci koyi ga dukkan musulmi da wadanda ba musulmi ba.

Ministan tsaron ya bukaci Al’ummar musulmi dasu yi amfani da wanna biki wajen rokowa kasar kyakkyawar makoma, ta hanyan yi mata add’oin samun zaman lafiya mai dorewa, gami da kasancewa cikin masu bada gudunmawar da ta dace wajen magance kalubalen tsaron da kasar ke fama da shi, tare da shiga cikin masu samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, wanda shine tushen addinin Musulunci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp