Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta bukaci Al’ummar musulmi dasu yi amfani da lokacin bukukuwan maulidu wajen yiwa kasar Addu’ar kan matsalolin tsaron da suka addabi Al’ummar ta.
Wannna na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mataimaki na musamman ga Ministan tsaron Nijeriya Manjo Janar Bashir Salihi Magashi mai ritaya, kan harkokin sadarwa Mohammad Abdulkadri ya fitar domin taya Al’ummar Musulmi murnar Mauludin Fiyayyen Halitta na bana.
Read Also:
Yace haihuwar fiyayyen halitta ta zo wa da duniya da abubuwan da suka jibanci yadda za’ayi koyi da hakuri, addu’oi da Kankan da kai, gami da tsoron Allah, wadanda a cewar sa sun cancanci koyi ga dukkan musulmi da wadanda ba musulmi ba.
Ministan tsaron ya bukaci Al’ummar musulmi dasu yi amfani da wanna biki wajen rokowa kasar kyakkyawar makoma, ta hanyan yi mata add’oin samun zaman lafiya mai dorewa, gami da kasancewa cikin masu bada gudunmawar da ta dace wajen magance kalubalen tsaron da kasar ke fama da shi, tare da shiga cikin masu samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, wanda shine tushen addinin Musulunci.










