Home DUNIYA Rasha za ta Gina Babbar Cibiyar Tara Gas a Turkiya don Maye...

Rasha za ta Gina Babbar Cibiyar Tara Gas a Turkiya don Maye Gurbin NordStream

Shugaba Recep Tayyip Erdogan na Turkiya ya goyi bayan shirin takwaransa na Rasha Vladimir Putin game da gina babbar cibiyar tara iskar gas a cikin kasar bayan da shugaban ya bayyana cewa wannan dabara ce da ke bukatar a aiwatar da ita a cikin gaggawa.

Jaridu a Ankara sun ruwaito cewa tun farko shugaba Vladimir Putin ne ya gabatarwa Erdogan shirin, a wani yunkuri na isar da makamashi kudancin Turai ta cikin Turkiya sakamakon matsalar da ake samu a aikin tura iskar gas din ta bututun gas din NordStream.

Tuni dai wannan mataki ya ja hankalin kasashen Turai musamman Faransa inda ofishin shugaba Emmanuel Macron ya fitar da sanarwar da ke sukar matakin wanda ya bayyana yunkurin na Rasha da Turkiya a matsayin abin da ya sabawa hankali.

Rasha wadda dama ita ke bai wa Turkiya makamashin gas ta hanyar bututun TurkStream da ke karkashin bakin teku wanda ya hada kasashen biyu, sabon yunkurin zai saukaka mata fitar da gas zuwa kasashen Turai wadanda ta ke jituwa da su tare zagaye wadanda ta ke takun saka da su.

Erdogan da ke sanar da wannan sabon yunkuri bayan dawowarsa daga ganawa da Putin a Kazakhstan jiya alhamis, ya ce ko shakka babu za a samar da rumbunan adana gas din a mahadar kasashen Turkiya da Bulgaria da kuma Girka.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp