Shugaban kungiyar tarayya Afirka kuma shugaban kasar Senegal Macky Sall na Shirin halartar taron G20 da za a yi a Bali na kasar Indonisiya, kamar yadda jami’ai suka bayyana.
Sall zai kasance a taron da huluna biyu wato zai wakilci kungiyar AU da kuma kasarsa ta Senegal kamar yadda guda cikin jami’an ya shadawa kamfanin yada labarai na reuters a ranar juma’a.
Read Also:
Ziyarar ta Sall wadda it ace ta farko a taron G20, na zuwa ne a daidai lokacin da nahiyar afirka ke kokarin ganin ta rike kasashen masu karfin arziki domin yin la’akari da alkawuran da suka dauka na yanayi.
Hakan ya biyo bayan halarar sall taron sauyin yanayi na majalisa dinkin duniya na COP27 da aka gudanar a kasar Masar inda ya kasance babban mai bada shawara ga kasashe masu arziki da sub a da gudunmmawar tsabar kudi don taimakawa afirka ta daidaita sauyin yanayi.
Taron kasashen na G20 da zai gudana a garin bali na kasar Indonesiya, zai gudana ne a ranakun 15-16 ga watan Nuwamba, wanda ya mamaye mako biyu na taron COP27.
Africa News











