Home DUNIYA AU na shirin kakabawa Chadi Takunkumi

AU na shirin kakabawa Chadi Takunkumi

Kwamitin zaman lafiya da tsaro na Tarayyar Afirka (PSC) ya fara wani muhimmin taro kan kasar Chadi domin nazari kan wani rahoton shugaban kungiyar kan rikice-rikicen baya-bayan nan da suka wakana baya ga duba yiwuwar kakabawa kasar takunkumi.

Mambobi 15 na wannan kwamiti da ke da alhakin kariya da warware rikice-rikicen kasashen Afirka za su yi nazari kan rahoton da shugaban gudanarwarta dan asalin kasar Chadi Moussa Faki Mahamat ya gabatar, rahotan da tuni ya yadu a kafofin sada zumunta tun gabanin gabatar da shi.

Rahotan mai shafuka takwas ya tabbatar da sahihancin sa, bashi da wani sauki ga mahuntan rikon kwaryar sojin Chadi karkashin jagorancin janar Mahamat Idriss Deby Itno.

Rahotan ya zargi gwamnatin rikon kwaryar Chadi da kin mutunta wa’adin watanni 18 na mika mulki ga fararen hula kamar yadda aka yi alkawari tun farko, kana sunyi biris da mutunta haramcin da aka sanya wa sojojin da ke kan mulki shiga takara a zabe mai zuwa, abin da shugaban hukumar ta AU Moussa Faki ke ganin biri ne yayi kama da mutun, don haka babu wani zabi face kakaba musu takunkumi.

Tuni wata majiya mai tushe ta tabbatar da fushin Ndjamena tun bayan yaduwar rahoton, inda suka ce kungiyar ci gaban tattalin arzikin kasashen Tsakiyar Afirka ke bibiyar lamuran ba hurumin AU ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp