Home DUNIYA WHO: Ebola ta Kashe Mutu 54 a kasar Uganda

WHO: Ebola ta Kashe Mutu 54 a kasar Uganda

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta ce cutar Ebola ta kashe mutane da yawansu ya kai 54 cikin kwanaki 55 da bullarta a Uganda, dai dai lokacin da ake ci gaba da samun karuwar masu harbuwa da cutar.

Cikin rahoton da WHO ta fitar kan yadda cutar ta Ebola ke ci gaba da lakume rayuka a Uganda, ta ce yankin Mubende da ke tattara alkaluman na da mutane 29 cikin mutanen 54 da cutar ta kashe.

A cewar rahoton daga lokacin da cutar ta bulla a ranar 20 ga watan Satumba zuwa yanzu an samu mutane 137 da aka tabbatar sun kamu da ita yayinda wasu 65 kuma suka warke.

Hukumar ta WHO ta ce yankunan da cutar ta fi yaduwa a sassan Uganda sun kunshi Kassanda da Kyegegwa da kuma Kagadi baya ga Bunyangabu da Wakiso da kuma Masaka da Kampala.

WHO ta ce yankunan Mubende da Kassanda inda ta fi tsananta na jumullar mutum 63 da kuma 47 da zuwa yanzu ke jinyar cutar ta Ebola.

Dukkanin yankunan dai yanzu haka na karkashin killacewar kwanaki 21 a kokarin dakile yaduwar cutar, wanda ya sa tun daga ranar 10 ga watan nan ba a sake samun wanda ya harbu ba.

Cikin mutane dubu 2 da 187 da aka yi imanin sun yi mu’amala da masu dauke da cutar, sun kammala killacewar kwanaki 21 karkashin kulawar jami’an lafiya kuma mutum 1 da 908 basu harbu da cutar ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp