Home General Rundunar ‘yan sanda Nijeriya  zata Girke Jami’anta a Kan haryar jirgin kasan...

Rundunar ‘yan sanda Nijeriya  zata Girke Jami’anta a Kan haryar jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna

Za’a girke Jami’an ‘yan sanda, biyo bayan dawo da jigilar fasinjoji a jirgin kasa daga Abuja zuwa kaduna.
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan na kasa CSP Olumuyiwa Adejobi, mnipr, mipra ya fitar a birnin tarayyar kasar Abuja mai dauke da kwanan watan 4 ga watan Disamba 2022 da aka akewa PRNigeria.
Sanarwar tace babban sefeton ‘Yan sanda Nijeriya Usman Alkali Baba, psc(+), NPM, NEAPS, fdc, CFR, ya bada umarnin girki Jami’an kwantar da tarzoma na Mobile Force, K-9, Force na kwarru da kuma Jami’an ‘yan sandan layin dogo domin gudanar da ayyukan tsaro kan hanyar jirgin kasan daga Abuja zuwa Kaduna ranar litinin 5 ga Disambar 2022.
Inda sanarwa ta kara da cewa Rundunar ‘yan sandan Nijeriya na cigaba da tattaunawa da hukumar dake lura da Jiragen Kasan Nijeriya da sauran Jami’an tsaro domin gudanar da aikin tsaron Al’umma yadda ya kamata.
Dakarun zasu lura da muhimman wuraren na tashar jirgin kasar da hanyar da yake bi da kuma bada shawarwari don samar da ingantacce tsaro ga fasinjoji da dukiyoyin su ta hanyar kare su ga dukkan abinda kaje kazo
Babban Sifeton ‘yan sanda ya kuma tabbarwa da Al’umma kasar musamman fasinjojin jirgin kasar cewa zasu kare su da lafiyar su da dukiyar su da zarar sun hau kan hanya domin yin balaguro, dama sauran fasinjojun dake kan jirgin kasa a dukkan fadin kasar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp