Home General Bikin Kirsimeti da Sabuwar Shekara: FRSC zata girke jami’ai sama da  Dubu ...

Bikin Kirsimeti da Sabuwar Shekara: FRSC zata girke jami’ai sama da  Dubu  36 a Sassa Nijeriya

Bikin Kirsimati da Sabuwar Shekara: FRSC zata girke jami’ai sama da  Dubu  36 a Sassa Nijeriya

Hukumar kiyaye hadurra a Najeriya FRSC, ta sanar da aike jami’anta a sassa daban-daban na kasar domin gudanar da sintiri a tituna yayin gudanar da bukukuwan Kirismeti da na sabuwar shekara da ke tafe.

Wannan na cikin jawabin da mukaddashin shugaban hukumar , Dauda Biu ya yi a yayin da yake ganawa da manema labarai a ranar Litinin, ya ce sun tanadi  jami’ai 36,224 da za su yi wannan aikin.

Sai dai ya ce hukumar na bai wa ‘yan Najeriya tabbacin kare lafiyarsu da dukiya a lokacin da ake gudanar da bukukuwan na  karshen shekarar 2022 lafiya da fatan ganin 2023 da ke tafe.

A Najeriya dai ana yawan samun hadurran motoci a manya da kananan titunan kasar, musamman lokacin bukukuwan karshen shekara.

Hukumar kiyaye hadurra ta kasar da ‘yan sanda na dora alhakin hadurran ababen hawan kan tukin ganganci, ko gudu fiye da kima da direbobi ke yi, sai kuma rashin hakurin masu ababen hawa a lokacin da aka samu cunkoun ababen hawa.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp