Home DUNIYA Fada ya kaure tsakanin sojojin Sudan da runduna ta musamman

Fada ya kaure tsakanin sojojin Sudan da runduna ta musamman

An ji karar fashe fashe a babban birnin Sudan, Khartoum a yau Asabar, sakamakon rikicin da ya kaure tsakanin dakaru na musamman da ke gadin fadar shugaban kasar da sojoji, kwanaki bayan da rundunar sojin kasar ta yi kashedin cewa kasar ta shiga wani matsayi mai hatsari.

Rikicin ya  barke ne  bayan da aka shafe makwanni ana zaman tankiya tsakanin jagoran gwamnatin sojin kasar, Janar Abdel Fattah al-Burhan da mataimakinsa, kuma kwamandan runduna ta musamman na kasar, Hamdan Daglo.

Ganau sun ruwaito cewa an yi arangama, inda aka ji karar fashe fashe a kusa da ofishin runduna ta musamman, wato RSF.

Runduna ta musamman ta ce dakarunta sun karbe iko da filin jirgin sama na birnin Khartoum a halin da ake ciki, bayan da shaidu suka ce sun hango motoci cike da mayaka na shiga cikin harabar filin jirgin saman.

sun ruwaito cewa sun jiyo karar  harbe harbe a kusa da filin jirgin saman, da kuma kusa da gidan Burhan a arewacin birnin Khartoum.

An hango fararen hula suna ta tserewa don tsira da rayukansu.

Bangarorin biyu dai na zargin jina da  tada rikicin.

Jagoran mulkin sojin Sudan, Burhan da mataimakainsa suna cikin rashin jituwa ne a kan tattaunawar yarjejeniyar mika mulki ga farar hula tare da karshen rikicin da ya kunno kai tun bayan juyin mulkin shekarar 2021.

Runduna ta musamman ta RSF da aka kirkiro  a shekarar 2013 ta sao asali ne daga kungiyaar ‘yaan tsagerar Janjaweed, wadda tsohon shugaban kasar, Omar al-Bashir ya yi amafani da ita wajen muzgunawa ‘yan tsirarun kabilu wadanda ba Larabawa ba a yankin yammacin Darfur, lamarin da yanzu ya janyo masa tuhumar aikata laifukan yaki.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp