Home DUNIYA Sama da Mutane dubu 3 sun rasa muhallin su a kasar Sudan

Sama da Mutane dubu 3 sun rasa muhallin su a kasar Sudan

Majalisar Dinkin Duniya ta ce mutane sama da 400 suka mutu ya zuwa wannan lokaci a rikicin kasar Sudan, yayin da sama da 3,500 suka samu raunuka daban daban.

Majlisar ta kuma kara da cewa daga cikin mutanen da suka mutu akwai yara kanana guda 9, bayan sama da 50 da suka jikkata.

Mai Magana da yawun hukumar lafiya ta duniya Margareth Harris ce ta gabatar da wadannan alkaluma masu tada hankali, sakamakon rahotannin da suke tattarawa daga hannun hukumomin lafiyar Sudan.

Harris ta ce yanzu haka asibitocin kula da lafiyar jama’a guda 20 sun daina aiki a Sudan saboda tashin hankalin, yayin da wasukarin 12 ke fuskantar barazanar dakatar da aikace aikacensu, wanda ake ganin na iya haifar da karin illa ga jama’a.

Shima mai Magana da yawun Hukumar da ke kula da kananan yara ta Majalisar wato UNICEF, James Elder ya ce rufe asibitocin ba wai kawai zai shafi wadanda suka samu raunuka sakamakon wannan tashin hankalin bane, har ma da marasa lafiyar da ke bukatar kulawa.

Elder ya ce dama kasar Sudan na daya daga cikin kasashen da ke da yawan yara masu fama da tamowa, kuma ganin yadda wannan rikici yayi kamari, ana iya samun karin yara kusan dubu 50 da za su fuskanci wannan matsala.

Rahotanni sun ce har a yau da juma’a ke bikin Sallar Idi, ana ta yin barín wuta tsakanin bangarorin biyu da ke kokawar mulki a cikin kasar.

Kungiyar likitoci ta kasa ta ce daren jiya anyi ta jin karar fashewar bama bamai da kuma amon makaman atilare a birnin Khartoum, yayin da sojojin gwamnati da na kungiyar RSF ke musayar wuta da bindigogi a tsakaninsu.

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres tare da Sakataren harkokin wajen Amurka Antonio Blinken sun bukaci tsagaita wuta na tsawon kwanaki 3 domin bai wa jama’a damar gudanar da bukukuwan Sallah.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp