Home Labarai Karo na Biyu: Shugaba Buhari ya ɗage Kidayar 2023

Karo na Biyu: Shugaba Buhari ya ɗage Kidayar 2023

President-Muhammadu-Buhari

Karo na Biyu: Shugaba Buhari ya ɗage Kidayar 2023

A karo na biyu, shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya ɗage kidayar 2023 da aka shirya gudanarwa a Najeriya.

Ya ɗauki wannan matakin ne bayan ganawa da shugaban NPC na ƙasa, Nasir Isa-Kwarra, da tawagarsa a fadar shugaban ƙasa.

A halin yanzun, Buhari ya bar wuƙa da nama hannun gwamnati mai zuwa karƙaashin Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.

Abuja – Shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya amince da sake ɗaga aiki kidayar mutane da gidaje a Najeriya na shekarar 2023.

Jaridar ta ce shugaban ƙasan ya ɗage aikin kidayar wanda aka tsara gudanarwa ranar 3 zuwa 7 ga watan Mayu, 2023, a yanzu ya bar wuƙa da nama hannun sabuwar gwamnati.

Buhari ya ɗauki wannan matakin ne a wurin ganawa da wasu mambobin majalisar zartaswa da shugaban hukumar kidaya ta ƙasa (NPC), Nasir Isa-Kwarra, da tawagarsa a Abuja ranar Jummu’a.

Wannan na ƙunshe a wata sanarwa da aka rabawa manema labarai da safiyar Asabar mai ɗauke da sa hannun Ministan yaɗa labarai, Alhaji Lai Muhammed.

Sanarwan ta ce:

“Yayin da aka cimma matsayar sake ɗage aikin kidayar, taron ya kara jaddada muhimmancin kidayar yan Najeriya da gidaje, shekaru 17 bayan gudanar da kidaya a Najeriya.”

“Hakan ne kaɗai zai sa a tattara bayanai waɗanda zasu taimaka wajen cika burin kawo ci gaba a ƙasar nan kuma ya daidaita walwaha a rayuwar mazauna Najeriya.”

A wurin taron, an ji shugaba Muhammadu Buhari na cewa an cimma nasarori masu yawa a shirye-shiryen gudanar da kidaya, wacce aka ɗaga yanzu.

Ya kuma yaba wa hukumar kidaya ta ƙasa NPC bisa yadda ta ɗauki tsaruka da hanyoyin gudanar da sahihiyar kidaya wacce za’a dogara da ita a gwamnatance.

Jiga-jigan da suka halarci zaman Manyan kusoshin gwamnati da suka je wurin taron sun kunshi, Antoni Janar kuma ministan shari’a, Abubakar Malami, ministan yaɗa labarai, Lai Muhammed, Ministar kudi, kasafi da tsare-tsaren ƙasa, Zainab Ahmed.

Sauran su ne, ƙaramin ministan kasafi da tsare-tsaren ƙasa, Mista Clem Agba, da kuma Sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha, kamar yadda Channels tv ta ruwaito.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp