Home Labarai An kama ‘yan daba da masu ƙwacen waya 98 a Kaduna

An kama ‘yan daba da masu ƙwacen waya 98 a Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna ta tabbatar da kama ‘yan daba da masu ƙwacen wayoyi da aka fi sani da ‘yan ‘Sara-Suka’ 98 a jihar.

Gwamnan jihar Mallam Nasir El-Rufai ne ya buƙaci ɗaukar tsattsauran mataki kan ɓata-garin, sakamakon ƙaruwar ayyukan ‘yan daba da masu ƙwacen wayoyi a ƙwaryar birnin Kaduna.

Cikin wata sanarwa da kwamishinan tsaro da al’amuran cikin gida na jihar Samuel Aruwan ya fitar ya ce an gurfanar da 19 daga cikinsu a gabon kotu, yayin da ake ci gaba da bincike kan mutane 61, kafin a gurfanar da su.

Ɓata-garin kan farmaki mutane tare da ƙwace musu wayoyi da sauran kayayyaki, lamarin da ya yi sanadiyyar rasa rayuka tare da jikkata mutane masu yawa.

Rahoton kamen wanda ‘yan sanda suka fitar, ya ce an kama ‘yan dabar a ranakun 26 da 28 ga watan Afrilu.

Rahoton ya ce 18 daga cikin ɓata-garin an kai su sashen binciken manyan laifuka na rundunar ‘yan sandan jihar domin faɗaɗa bincike, gabanin gurfanar da su a gaban kotu.

Gwamnan jihar ya umarci rundunar ‘yan sandan da su tabbatar da yin abin da ya dace domin gurfanar da su a gaban kotu, tare da faɗaɗa bincike don kamo duk masu aikata irin wannan ta’asa a faɗin jihar.

El-Rufai ya kuma jajanta wa iyalan waɗanda suka rasa rayukansu, tare da fatan samun sauƙi ga waɗanda suka jikkata, sanadiyyar ayyukan ‘yan bindigar.

Daga ƙarshe gwamnan ya yi kira ga al’umma musamman mazauna unguwannin da ake wannan ta’asa da su kai sunayen ‘yan dabar da ke addabar yankunansu ga jami’an tsaro domin a bibiye su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp