Tinubu ya kaddamar da majalisar tattalin arzikin Nigeria

Shugaban kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ƙaddamar da majalisar tattalin arzikin kasa (NEC).

An kaddamar da majalisar ne ƙarƙashin jagorancin mataimakin shugaban ƙasar Sanata Kashim Shettima a zauren majalisar da safiyar ranar Alhamis.

A wani saƙo da Dada Olusegun, mataimaki na musamman ga shugaban ƙasar ya wallafa a shafinsa na twitter, ya ce an ƙaddamar da majalisar ne a zaurenta da ke fadar shugaban ƙasa a Abuja..

A Ƙwarya-ƙwaryar bikin ya samu halartar shugaban ma’aikata na fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila, da Sakataren gwamnatin tarayya (SGF), Sanata George Akume da gwamnonin jihohin ƙasar 36.

Da yake jawabi a lokacin ƙaddamar da majalisar, shugaban ƙasar ya buƙaci gwamnonin su haɗa kai, wajen bunƙasa ƙananan hukumomi da ababen more rayuwa, duba da manyan ƙalubalen da ƙasar ke fuskanta.

“Ni da ku duk muna buƙatar hakan, kan haka muka gudanar da yakin neman zaɓukanmu, har ma muka yi rawa a gaban jama’a don jaddada alƙawuranmu, don haka, ba mu da dalilin yin korafi kan haka. ‘Yan Najeriya na nuna mana goyon baya. Suna son gyara kuma suna son hakan cikin gaggawa”.

PRNigeria hausa

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 33 minutes 50 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 15 minutes 15 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com