Home DUNIYA Matakin Soji zai zama na karshe kan sojojin Nijar – Manyan Hafsoshin...

Matakin Soji zai zama na karshe kan sojojin Nijar – Manyan Hafsoshin ECOWAS

Manyan hafsoshin tsaron ƙungiyar Ecowas za su samar da mafita idan dukkan hanyoyin da aka bi a siyasance ba su yi tasiri ba bayan juyin mulki a Nijar.

Mai magana da yawun rundunar sojin Najeriya, Birgediya JanarTukur Gusau ya bayyana hakan jim kadan bayan kammala taron da suka gudanar, in da yace matakin soji zai zamo na karshe.

“Matakin soji zai zama na ƙarshe da za a ɗaukar kan dakarun sojojin da suka yi Juyin Mulki a kasar, ”

Manyan hafsoshin tsaron ƙungiyar ta raya tattalin arzikin ƙasashen Afirka ta Yamma na tattaunawa a Abuja daga yau Laraba zuwa Juma’a domin tattaunawa kan hanyoyin da za a bi wajen shawo kan sojojin da suka yi juyin mulkin, inda aka hamɓarrar da gwamnatin Shugaba Mohamed Bazoum a makon da ya gabata.

Manyan hafsoshin tsaron Ghana, da Najeriya, da Benin, da Togo, da Saliyo, da Laberiya, da Gambiya, da Cote D’Ivoire, da Cape Verde ne ke halartar taron.

Sai dai takwarorinsu na Mali, da Nijar, da Guinea Bissau, da Burkina Faso, da Guinea ba su halarta ba sakamakon dakatar da su da Ecowas ta yi daga ƙungiyar saboda juyin mulkin da suka jagoranta a ƙasashensu.

Manyan hafsoshin tsaron za su gabatar da matakin da suka cimma ga shugaban ƙungiyar Bola Tinubu a ranar Juma’a.

Daga nan ne shugaban ƙungiyar zai yanke shawara kan mataki na gaba da za a ɗauka kan sojojin ƙarƙashin jagorancin Janar Abdourahmane Tchiani, wanda ya ayyana kan sa a matsayin shugaban Nijar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp