Home DUNIYA Sojojin ECOWAS sun kagu su kaddamar da Matakin soji kan Jamhuriyar Nijar

Sojojin ECOWAS sun kagu su kaddamar da Matakin soji kan Jamhuriyar Nijar

Ƙasashen Yammacin Afrika sun amince da wani tsari na ɗaukar matakin soji kan Nijar, idan har sojojin da suka yi juyin mulki suka ƙi amincewa da sharaɗin dawo da hamɓarren shugaba, Mohamed Bazoum bisa karagar mulkin.

Tun da farko ECOWAS ta bai wa sojojin na jamhuriyar Nijar wa’adin ranar Lahadi su mayar da mulki ga farar hula.

Alamu na nuna cewa sojojin Ecowas sun ƙagu da su ƙaddamar da yaƙi a Nijar idan har hakan ya zama dole.

Yanzu haka dai, Najeriya ta rufe iyakokin ƙasar da Nijar, ta kuma yanke wutar da take bai wa Nijar din duk a lokaci guda, matakan sun haddasa tashin farashin kayan masarufi a ƙasar, hakan na nuna yadda matakan Ecowas ɗin za su haddasa wahalhalu ga ƴan ƙasar.

A ranar Alhamis wata tawaga ta kungiyar ta je Nijar, domin shiga tsakani sai dai ba ta samu damar ganawa da shugaban mulkin sojin ba, da ma hamɓararren shugaban na farar hula.

Masu aiko da rahotanni sun ce, ɗaukar matakin soji kan lamarin zai iya zama mai wahala sosai, saboda kayan aiki, da kuma hadari, domin zai iya kara dagula al’amura a yankin, wanda masu ikirarin jihadi ke yi wa ta’annati.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp